TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: Shin ‘yan ta’adda sun yi barazanar jefa bama-bamai a coci a 2022? A’a, bidiyo na hoto ya tsufa
Share
Latest News
FACT CHECK: Did lawmakers skip the national anthem during Tinubu’s Democracy Day speech?
FACT CHECK: Did a military coup oust Paul Biya as Cameroon’s president?
FACT CHECK: Ndume erred. 22 governors didn’t endorse Jonathan in 2015
Rárá, Pope Leo kò bẹ Tinubu kó tú Nnamdi Kanu sílẹ̀ ní àtìmọ́lé
Ḿbà, Pope Leo áyọghị Tinubu kà ọ́ tọ́pụ̀ Nnamdi Kanu nà ǹgá
No, Pope Leo no beg Tinubu to release Nnamdi Kanu
A’a, Paparoma Leo bai nemi Tinubu ya saki Nnamdi Kanu ba
FACT CHECK: No, Pope Leo didn’t ask Tinubu to release Nnamdi Kanu
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

Shin ‘yan ta’adda sun yi barazanar jefa bama-bamai a coci a 2022? A’a, bidiyo na hoto ya tsufa

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published June 17, 2022 4 Min Read
Share

Wani bidiyo dake nuna Ayuba Elkana, kwamishinan yan sanda na jihar Zamfara, yana shaida cewar sun samu wata wasikar barazana daga wurin yan ta’adda dake umurtar mabiya addinin Kirista dake jihar Zamfara dasu rufe duka cocunan dake jihar na tsawon wata uku na ta yaďuwa a shafukan sada zumunta.

An tura bidiyon a shafin Facebook, Twitter da Whatsapp.

“Yan sanda sun tabbatar da sun samu wasikar barazana dake umurtan mabiya addinin Kirista dasu rufe cocunan dake Nijeriya na tsawon wata uku”, rubutun da wani yayi a karkashin bidiyon kenan a shafin sa na Facebook a ranar 14 ga watan Yuni.

Shafin Facebook din yana da Mabiya sama da dubu dari da sha biyu (112,000). Mutane sama da dubu dari da sittin da biyar (165,000) sun kalla bidiyon, da kuma mutane sama da dari bakwai da hamsin (750) sun yi sharhi akai sannan mutane sama da dubu takwas da dari biyu (8,200) sun tura bidiyon.

Sharhin da akayi a karkashin bidiyon dakuma labarin dayake dauke da, ya nuna cewa mutane da yawa sun gamsu da abin da suka gani.

TABBATARWA

Wani bincike da TheCable ya yi ya nuna cewa bidiyon da ke yawo ya tsufa kuma an yi shi a cikin 2021.

Anyi bidiyon a jihar Zamfara, inda Elkana ya gana da manema labarai a ranar 30 ga watan Nuwamban 2021. Yayin da yake ganawa da manema labarai a garin Gusau, babban birnin jihar, Elkana ya shaida wa manema labarai cewa yan sanda sun samu wasikar barazana daga yan ta’adda dake umurtan mabiya addinin Kirista dasu rufe cocunan dake jihar na tsawon shekara uku, ko kuma sun fuskanci barazanar harin da ze biyo baya.

“An ajiye wasikar ne a kofar shiga ofishin yan sandan jihar” inji kwamishinan yan sandan jihar.

Yayin da yake magana akan shirye-shiryen da jami’an tsaro keyi akan matsalar tsaro, kwamishinan yace wasikar na dauke da sunayen wasu cocuna dake waje-wajen babban birnin jihar da za a kai wa hare-hare lokacin da ake cikin bauta kafun karshen shekarar 2021.

Jaridar TheCable ta tuntubi Iliya Tsiga, shugaban kungiyar kiristoci ta kasa (CAN) reshen jihar Zamfara, yace bidiyon dake yawo tsohon bidiyo ne.

“Naga bidiyon dakuke magana. Tsohon bidiyo ne tun watan Nuwamban 2021. Ana sake yaďa shi ne. Wannan batun an riga da an shawo kanshi; kuma wanda ya tura wannan bidiyon kawai yana neman tayar da zaune tsaye ne,” inji Tsiga.

“Wasikar an yi shi ne a matsayin barazana ga duka mabiya addinin Kirista dake jihar. Basu bayyana wata kabila ba. Muna kira ga jama’a dasu yi watsi da bidiyon da hoton kuma su ci gaba da harkoki da alamuran rayuwa na yau da kullun”.

HUKUNCI

Bidiyon dake yawo tsohon bidiyo ne tun shekarar 2021, labarin da yake dauke da shi da ke cewa yan ta’adda sun umarci a rufe cocuna a fadin kasar nan na tsawon wata uku ba gaskiya bane.

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi June 17, 2022 June 17, 2022
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

FACT CHECK: Did lawmakers skip the national anthem during Tinubu’s Democracy Day speech?

A viral X post claims that Nigeria’s new national anthem was not recited during the…

June 13, 2025

FACT CHECK: Did a military coup oust Paul Biya as Cameroon’s president?

Reports of a military coup in Cameroon ousting President Paul Biya have gone viral on…

June 13, 2025

FACT CHECK: Ndume erred. 22 governors didn’t endorse Jonathan in 2015

On June 8, Ali Ndume, senator representing Borno south, claimed that 22 governors elected on…

June 10, 2025

Rárá, Pope Leo kò bẹ Tinubu kó tú Nnamdi Kanu sílẹ̀ ní àtìmọ́lé

Ẹni kan tí ó ń lo Facebook, ohun ìgbàlódé ibaraẹnisọrẹ orí ayélujára sọ pé Robert…

June 10, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Rárá, Pope Leo kò bẹ Tinubu kó tú Nnamdi Kanu sílẹ̀ ní àtìmọ́lé

Ẹni kan tí ó ń lo Facebook, ohun ìgbàlódé ibaraẹnisọrẹ orí ayélujára sọ pé Robert Francis Prevost, Pope Leo XIV…

CHECK AM FOR WAZOBIA
June 10, 2025

Ḿbà, Pope Leo áyọghị Tinubu kà ọ́ tọ́pụ̀ Nnamdi Kanu nà ǹgá

Ótù onye na Facebook ekwuola na Pope Leo na ụfọdụ ndị Bishop yọrọ onye isiala Bola Tinubu ka ọ tọpụ…

CHECK AM FOR WAZOBIA
June 10, 2025

No, Pope Leo no beg Tinubu to release Nnamdi Kanu

One Facebook user claim sey Pope Leo XVI and oda bishops join mouth beg President Bola Tinubu to release Nnamdi…

CHECK AM FOR WAZOBIA
June 10, 2025

A’a, Paparoma Leo bai nemi Tinubu ya saki Nnamdi Kanu ba

Wani mai amfani da Facebook ya yi ikirarin cewa Paparoma Leo na 16 da wasu limaman coci sun roki shugaban…

CHECK AM FOR WAZOBIA
June 10, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?