TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: Shin ‘yan ta’adda sun yi barazanar jefa bama-bamai a coci a 2022? A’a, bidiyo na hoto ya tsufa
Share
Latest News
Ókwú Badenoch nà ụ́mụ̀ yá ápụ̀ghị̀ ínwétá íkíké ị́bụ ńdị́ Naijiria bụ̀ àsị́
Kemi Badenoch claim sey her children no fit get Nigerian citizenship but she no tok true
Irọ́ ni Kemi Badenoch pa pé òfin kò fààyè gba àwọn ọmọ òhun láti di ọmọ Nàìjíríà
Maganar Kemi Badenoch na cewa ‘ya’yanta ba za su iya samun shaidar zama dan Najeriya ba karya ne
FACT CHECK: Kemi Badenoch’s claim that her children can’t get Nigerian citizenship is false
Naijiria ọ̀ kàgbùrù ńkwékọ́rị́tá àzụ́máhị́á àkụ̀ ọ̀nàtàràchí yá nà US nwèrè n’íhì ḿmáchí visa?
Ǹjẹ́ Nàìjíríà dá àjọṣe lórí àwọn àlùmọ́ọ́nì láàárín òhun àti Amẹ́ríkà dúró nítorí visa?
Nigeria stop ‘mineral deal’ with US afta visa restriction?
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

Shin ‘yan ta’adda sun yi barazanar jefa bama-bamai a coci a 2022? A’a, bidiyo na hoto ya tsufa

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published June 17, 2022 4 Min Read
Share

Wani bidiyo dake nuna Ayuba Elkana, kwamishinan yan sanda na jihar Zamfara, yana shaida cewar sun samu wata wasikar barazana daga wurin yan ta’adda dake umurtar mabiya addinin Kirista dake jihar Zamfara dasu rufe duka cocunan dake jihar na tsawon wata uku na ta yaďuwa a shafukan sada zumunta.

An tura bidiyon a shafin Facebook, Twitter da Whatsapp.

“Yan sanda sun tabbatar da sun samu wasikar barazana dake umurtan mabiya addinin Kirista dasu rufe cocunan dake Nijeriya na tsawon wata uku”, rubutun da wani yayi a karkashin bidiyon kenan a shafin sa na Facebook a ranar 14 ga watan Yuni.

Shafin Facebook din yana da Mabiya sama da dubu dari da sha biyu (112,000). Mutane sama da dubu dari da sittin da biyar (165,000) sun kalla bidiyon, da kuma mutane sama da dari bakwai da hamsin (750) sun yi sharhi akai sannan mutane sama da dubu takwas da dari biyu (8,200) sun tura bidiyon.

Sharhin da akayi a karkashin bidiyon dakuma labarin dayake dauke da, ya nuna cewa mutane da yawa sun gamsu da abin da suka gani.

TABBATARWA

Wani bincike da TheCable ya yi ya nuna cewa bidiyon da ke yawo ya tsufa kuma an yi shi a cikin 2021.

Anyi bidiyon a jihar Zamfara, inda Elkana ya gana da manema labarai a ranar 30 ga watan Nuwamban 2021. Yayin da yake ganawa da manema labarai a garin Gusau, babban birnin jihar, Elkana ya shaida wa manema labarai cewa yan sanda sun samu wasikar barazana daga yan ta’adda dake umurtan mabiya addinin Kirista dasu rufe cocunan dake jihar na tsawon shekara uku, ko kuma sun fuskanci barazanar harin da ze biyo baya.

“An ajiye wasikar ne a kofar shiga ofishin yan sandan jihar” inji kwamishinan yan sandan jihar.

Yayin da yake magana akan shirye-shiryen da jami’an tsaro keyi akan matsalar tsaro, kwamishinan yace wasikar na dauke da sunayen wasu cocuna dake waje-wajen babban birnin jihar da za a kai wa hare-hare lokacin da ake cikin bauta kafun karshen shekarar 2021.

Jaridar TheCable ta tuntubi Iliya Tsiga, shugaban kungiyar kiristoci ta kasa (CAN) reshen jihar Zamfara, yace bidiyon dake yawo tsohon bidiyo ne.

“Naga bidiyon dakuke magana. Tsohon bidiyo ne tun watan Nuwamban 2021. Ana sake yaďa shi ne. Wannan batun an riga da an shawo kanshi; kuma wanda ya tura wannan bidiyon kawai yana neman tayar da zaune tsaye ne,” inji Tsiga.

“Wasikar an yi shi ne a matsayin barazana ga duka mabiya addinin Kirista dake jihar. Basu bayyana wata kabila ba. Muna kira ga jama’a dasu yi watsi da bidiyon da hoton kuma su ci gaba da harkoki da alamuran rayuwa na yau da kullun”.

HUKUNCI

Bidiyon dake yawo tsohon bidiyo ne tun shekarar 2021, labarin da yake dauke da shi da ke cewa yan ta’adda sun umarci a rufe cocuna a fadin kasar nan na tsawon wata uku ba gaskiya bane.

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi June 17, 2022 June 17, 2022
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

Ókwú Badenoch nà ụ́mụ̀ yá ápụ̀ghị̀ ínwétá íkíké ị́bụ ńdị́ Naijiria bụ̀ àsị́

Kemi Badenoch, onye ndú òtù Conservative Party nke obodo United Kingdom, ekwuola na ọ gaghị…

July 22, 2025

Kemi Badenoch claim sey her children no fit get Nigerian citizenship but she no tok true

Kemi Badenoch, leader of di United Kingdom Conservative Party, claim sey she no fit pass…

July 22, 2025

Irọ́ ni Kemi Badenoch pa pé òfin kò fààyè gba àwọn ọmọ òhun láti di ọmọ Nàìjíríà

Kemi Badenoch, arábìnrin tó jẹ́ olórí ẹgbẹ́ òsèlú alátakò tí wọ́n ń pè ní Conservative…

July 22, 2025

Maganar Kemi Badenoch na cewa ‘ya’yanta ba za su iya samun shaidar zama dan Najeriya ba karya ne

Kemi Badenoch, shugabar jam'iyyar masu ra'ayin rikau ta Burtaniya, ta yi ikirarin cewa ba za…

July 22, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Ókwú Badenoch nà ụ́mụ̀ yá ápụ̀ghị̀ ínwétá íkíké ị́bụ ńdị́ Naijiria bụ̀ àsị́

Kemi Badenoch, onye ndú òtù Conservative Party nke obodo United Kingdom, ekwuola na ọ gaghị enyenwu ụmụ ya ikike ịbụ…

CHECK AM FOR WAZOBIA
July 22, 2025

Kemi Badenoch claim sey her children no fit get Nigerian citizenship but she no tok true

Kemi Badenoch, leader of di United Kingdom Conservative Party, claim sey she no fit pass her right of Nigerian citizenship…

CHECK AM FOR WAZOBIA
July 22, 2025

Irọ́ ni Kemi Badenoch pa pé òfin kò fààyè gba àwọn ọmọ òhun láti di ọmọ Nàìjíríà

Kemi Badenoch, arábìnrin tó jẹ́ olórí ẹgbẹ́ òsèlú alátakò tí wọ́n ń pè ní Conservative Party ní orílẹ̀ èdè United…

CHECK AM FOR WAZOBIA
July 22, 2025

Maganar Kemi Badenoch na cewa ‘ya’yanta ba za su iya samun shaidar zama dan Najeriya ba karya ne

Kemi Badenoch, shugabar jam'iyyar masu ra'ayin rikau ta Burtaniya, ta yi ikirarin cewa ba za ta iya mika hakkinta na…

CHECK AM FOR WAZOBIA
July 22, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?