TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: Shin ‘yan ta’adda sun yi barazanar jefa bama-bamai a coci a 2022? A’a, bidiyo na hoto ya tsufa
Share
Latest News
FACT CHECK: Is Nigeria 4th fastest-growing economy in the world in 2025?
FACT CHECK: How true are Obi’s claims about poverty rate in Nigeria, China and Indonesia?
FACT CHECK: No, Finnish court didn’t approve Simon Ekpa’s extradition to Nigeria
FACT CHECK: Is Cardinal Arinze eligible to be elected as the next Pope?
Rárá, Jonathan kò sọ pé Tinubu yóò se àṣeyọrí nínú ètò ìdìbò fún Ipò Ààrẹ ní ọdún 2027
A’a, Jonathan bai yi hasashen nasarar Tinubu a zaben shugaban kasa na 2027 ba
No, Jonathan no predict Tinubu victory for 2027 presidential election
Ḿbà, Jonathan ágbaghị àmà na Tinubu gà-èmérí ńtùlíáka ónyé ísíàlà ǹkè áfọ̀ 2027
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

Shin ‘yan ta’adda sun yi barazanar jefa bama-bamai a coci a 2022? A’a, bidiyo na hoto ya tsufa

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published June 17, 2022 4 Min Read
Share

Wani bidiyo dake nuna Ayuba Elkana, kwamishinan yan sanda na jihar Zamfara, yana shaida cewar sun samu wata wasikar barazana daga wurin yan ta’adda dake umurtar mabiya addinin Kirista dake jihar Zamfara dasu rufe duka cocunan dake jihar na tsawon wata uku na ta yaďuwa a shafukan sada zumunta.

An tura bidiyon a shafin Facebook, Twitter da Whatsapp.

“Yan sanda sun tabbatar da sun samu wasikar barazana dake umurtan mabiya addinin Kirista dasu rufe cocunan dake Nijeriya na tsawon wata uku”, rubutun da wani yayi a karkashin bidiyon kenan a shafin sa na Facebook a ranar 14 ga watan Yuni.

Shafin Facebook din yana da Mabiya sama da dubu dari da sha biyu (112,000). Mutane sama da dubu dari da sittin da biyar (165,000) sun kalla bidiyon, da kuma mutane sama da dari bakwai da hamsin (750) sun yi sharhi akai sannan mutane sama da dubu takwas da dari biyu (8,200) sun tura bidiyon.

Sharhin da akayi a karkashin bidiyon dakuma labarin dayake dauke da, ya nuna cewa mutane da yawa sun gamsu da abin da suka gani.

TABBATARWA

Wani bincike da TheCable ya yi ya nuna cewa bidiyon da ke yawo ya tsufa kuma an yi shi a cikin 2021.

Anyi bidiyon a jihar Zamfara, inda Elkana ya gana da manema labarai a ranar 30 ga watan Nuwamban 2021. Yayin da yake ganawa da manema labarai a garin Gusau, babban birnin jihar, Elkana ya shaida wa manema labarai cewa yan sanda sun samu wasikar barazana daga yan ta’adda dake umurtan mabiya addinin Kirista dasu rufe cocunan dake jihar na tsawon shekara uku, ko kuma sun fuskanci barazanar harin da ze biyo baya.

“An ajiye wasikar ne a kofar shiga ofishin yan sandan jihar” inji kwamishinan yan sandan jihar.

Yayin da yake magana akan shirye-shiryen da jami’an tsaro keyi akan matsalar tsaro, kwamishinan yace wasikar na dauke da sunayen wasu cocuna dake waje-wajen babban birnin jihar da za a kai wa hare-hare lokacin da ake cikin bauta kafun karshen shekarar 2021.

Jaridar TheCable ta tuntubi Iliya Tsiga, shugaban kungiyar kiristoci ta kasa (CAN) reshen jihar Zamfara, yace bidiyon dake yawo tsohon bidiyo ne.

“Naga bidiyon dakuke magana. Tsohon bidiyo ne tun watan Nuwamban 2021. Ana sake yaďa shi ne. Wannan batun an riga da an shawo kanshi; kuma wanda ya tura wannan bidiyon kawai yana neman tayar da zaune tsaye ne,” inji Tsiga.

“Wasikar an yi shi ne a matsayin barazana ga duka mabiya addinin Kirista dake jihar. Basu bayyana wata kabila ba. Muna kira ga jama’a dasu yi watsi da bidiyon da hoton kuma su ci gaba da harkoki da alamuran rayuwa na yau da kullun”.

HUKUNCI

Bidiyon dake yawo tsohon bidiyo ne tun shekarar 2021, labarin da yake dauke da shi da ke cewa yan ta’adda sun umarci a rufe cocuna a fadin kasar nan na tsawon wata uku ba gaskiya bane.

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi June 17, 2022 June 17, 2022
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

FACT CHECK: Is Nigeria 4th fastest-growing economy in the world in 2025?

A viral post claims, based on International Monetary Fund (IMF) projections, that Nigeria ranks fourth…

May 9, 2025

FACT CHECK: How true are Obi’s claims about poverty rate in Nigeria, China and Indonesia?

Peter Obi, Labour Party (LP) presidential candidate in the 2023 elections, sparked a debate with…

May 5, 2025

FACT CHECK: No, Finnish court didn’t approve Simon Ekpa’s extradition to Nigeria

On Tuesday, some social media users and blog sites made a post claiming that a…

April 24, 2025

FACT CHECK: Is Cardinal Arinze eligible to be elected as the next Pope?

A social media user has claimed that Francis Arinze, a Roman Catholic cardinal, is the…

April 21, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Rárá, Jonathan kò sọ pé Tinubu yóò se àṣeyọrí nínú ètò ìdìbò fún Ipò Ààrẹ ní ọdún 2027

Ní ọjọ́ ajé, ọ̀rọ̀ kan to sọ pé Goodluck Jonathan, Ààrẹ orílẹ̀ èdè Nàìjíríà tẹ́lẹ̀ sọ pé Ààrẹ Bọla Tinubu…

CHECK AM FOR WAZOBIA
April 20, 2025

A’a, Jonathan bai yi hasashen nasarar Tinubu a zaben shugaban kasa na 2027 ba

A ranar Talata ne wani rahoto da ke ikirarin cewa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya yi hasashen nasarar Shugaba…

CHECK AM FOR WAZOBIA
April 20, 2025

No, Jonathan no predict Tinubu victory for 2027 presidential election

On Tuesday, one report wey claim sey former President Goodluck Jonathan predict President Bola Tinubu victory for di 2027 presidential…

CHECK AM FOR WAZOBIA
April 20, 2025

Ḿbà, Jonathan ágbaghị àmà na Tinubu gà-èmérí ńtùlíáka ónyé ísíàlà ǹkè áfọ̀ 2027

N’ubọchị Tuesde, ozi na-ekwu na onye bụburu onye isiala Naijiria, bụ Goodluck Jonathan, gbara àmà na onyeisiala Bola Tinubu ga-emeri…

CHECK AM FOR WAZOBIA
April 19, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?