TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: ‘Shin ‘yan jam’iyyar APC ne kadai aka kai hari an Imo kamar yadda Uzodinma ya yi ikirari?
Share
Latest News
REVEALED: The social media accounts using AI videos to amplify pro-Traore propaganda
FACT CHECK: Is Nigeria 4th fastest-growing economy in the world in 2025?
FACT CHECK: How true are Obi’s claims about poverty rate in Nigeria, China and Indonesia?
FACT CHECK: No, Finnish court didn’t approve Simon Ekpa’s extradition to Nigeria
FACT CHECK: Is Cardinal Arinze eligible to be elected as the next Pope?
Rárá, Jonathan kò sọ pé Tinubu yóò se àṣeyọrí nínú ètò ìdìbò fún Ipò Ààrẹ ní ọdún 2027
A’a, Jonathan bai yi hasashen nasarar Tinubu a zaben shugaban kasa na 2027 ba
No, Jonathan no predict Tinubu victory for 2027 presidential election
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

‘Shin ‘yan jam’iyyar APC ne kadai aka kai hari an Imo kamar yadda Uzodinma ya yi ikirari?

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published January 11, 2023 4 Min Read
Share

Hope Uzodimma, gwamnan jihar Imo, ya ce ‘yan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da mutanen da ke kusa da gwamnatinsa ne kadai ke fama da hare-haren rashin tsaro a jihar.

Uzodimma ya kuma yi zargin cewa ‘yan siyasa ne ke haddasa rashin tsaro a jihar.

Gwamnan Imo ya yi wannan ikirarin ne a ranar Alhamis yayin wani shiri a gidan Talabijin na Channels.

Events of the past have shown clearly that politicians are the ones behind the insecurity in Imo State.

– Sen. Hope Uzodimma, Governor of Imo State.#CTVTweets pic.twitter.com/hW2Pc2vm14

— Channels Television (@channelstv) January 5, 2023

“A yau, a tattaunawar da na yi da masu ruwa da tsaki a jihar Imo, na bayyana karara cewa abubuwan da suka faru a baya sun nuna karara cewa wadanda ke haddasa rashin tsaro a jihar Imo ‘yan siyasa ne, kuma wannan rashin tsaro na siyasa ne.” Inji Uzodimma.

“Misali, a waccan jawabin da na yi, na fito da matsaya a fili cewa duk mutanen da aka kai wa hari a Jihar Imo, da gidajen da aka kona, ‘yan APC ne kuma na kusa da gwamnati na.

“Idan ka duba, babu wani dan wata jam’iyyar siyasa da aka kai wa hari a jihar Imo; babu wani dan jam’iyyar adawa da aka kona gidansa, kuma hakan ya ci gaba da faruwa.

“Kawai ka ambaci na tsohon gwamna Ikedi Ohakin, kwanaki uku bayan ya kira liyafar cin abinci na musamman na masu ruwa da tsaki na Imo, ya kuma karfafa masu gwiwa da su marawa gwamnatin APC baya, bayan kwana biyu, an kai masa hari tare da kashe bayanan tsaronsa.

Kun ambaci tsohon gwamna Ikedi Ohakin. Bayan kwanaki uku da ya kira liyafar cin abinci na musamman ga masu ruwa da tsaki na jihar Imo tare da karfafa masu gwiwa da su marawa gwamnatin APC baya, bayan kwana biyu aka kai masa hari kuma aka kashe masu tsaron shi.

“Don haka, na gabatar da wannan al’amari ga mutanen Imo, an kama wasu – wasu manya daga cikin masu laifin.

“Don haka na kalubalanci jami’an tsaro a jihar Imo da su gaggauta bayyana rahotan wannan bincike da kuma wadanda ke da hannu wajen kashe-kashen a jihar ta Imo.

“Kuma za su yi haka kawai. Ba zan yi riya game da hakan ba. Ba zan yi siyasa da tsaron jihar Imo ba.”

TABBATARWA

A makonnin baya-bayan nan ne dai jaridar TheCable jerin hare-hare kan kadarorin kuma ‘yan siyasa da ‘yan bindiga suka yi a jihar Imo.

A kwanakin baya ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari kan ayarin motocin Ikedi Ohakim, tsohon gwamnan Imo, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar jami’an ‘yan sanda hudu.

A watan Disambar 2022, wasu ‘yan bindiga sun bankawa wata kotun majistare dake karamar hukumar Owerri da wata babbar kotu dake karamar hukumar Orlu ta jihar Imo wuta cikin sa’o’i 24.

Haka kuma a watan Disambar 2022, wasu ‘yan bindiga sun kashe Christopher Eleghu, dan takarar jam’iyyar Labour Party (LP) a mazabar Onuimo a majalisar dokokin jihar Imo.

A ranar 12 ga watan Disamba ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari a ofishin hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) da ke Owerri, babban birnin jihar Imo.

HUKUNCI

Maganar da Uzodimma ya yi na cewa ‘yan jam’iyyar APC da makusantan gwamnatin sa ne kawai aka kaiwa hari ba daidai ba ne.

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari tare da kashe dan takarar majalisar wakilai na jam’iyyar Labour a mazabar Onuimo, Christopher Eleghu a gidansa da ke Imo.

TAGGED: APC, attack, Fact Check, Imo State, Insecurity, Uzodinma

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi January 11, 2023 January 11, 2023
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

REVEALED: The social media accounts using AI videos to amplify pro-Traore propaganda

Many social media accounts owned by young Africans have touted Ibrahim Traore, Burkina Faso's military…

May 17, 2025

FACT CHECK: Is Nigeria 4th fastest-growing economy in the world in 2025?

A viral post claims, based on International Monetary Fund (IMF) projections, that Nigeria ranks fourth…

May 9, 2025

FACT CHECK: How true are Obi’s claims about poverty rate in Nigeria, China and Indonesia?

Peter Obi, Labour Party (LP) presidential candidate in the 2023 elections, sparked a debate with…

May 5, 2025

FACT CHECK: No, Finnish court didn’t approve Simon Ekpa’s extradition to Nigeria

On Tuesday, some social media users and blog sites made a post claiming that a…

April 24, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Rárá, Jonathan kò sọ pé Tinubu yóò se àṣeyọrí nínú ètò ìdìbò fún Ipò Ààrẹ ní ọdún 2027

Ní ọjọ́ ajé, ọ̀rọ̀ kan to sọ pé Goodluck Jonathan, Ààrẹ orílẹ̀ èdè Nàìjíríà tẹ́lẹ̀ sọ pé Ààrẹ Bọla Tinubu…

CHECK AM FOR WAZOBIA
April 20, 2025

A’a, Jonathan bai yi hasashen nasarar Tinubu a zaben shugaban kasa na 2027 ba

A ranar Talata ne wani rahoto da ke ikirarin cewa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya yi hasashen nasarar Shugaba…

CHECK AM FOR WAZOBIA
April 20, 2025

No, Jonathan no predict Tinubu victory for 2027 presidential election

On Tuesday, one report wey claim sey former President Goodluck Jonathan predict President Bola Tinubu victory for di 2027 presidential…

CHECK AM FOR WAZOBIA
April 20, 2025

Ḿbà, Jonathan ágbaghị àmà na Tinubu gà-èmérí ńtùlíáka ónyé ísíàlà ǹkè áfọ̀ 2027

N’ubọchị Tuesde, ozi na-ekwu na onye bụburu onye isiala Naijiria, bụ Goodluck Jonathan, gbara àmà na onyeisiala Bola Tinubu ga-emeri…

CHECK AM FOR WAZOBIA
April 19, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?