TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: ‘Shin ‘yan jam’iyyar APC ne kadai aka kai hari an Imo kamar yadda Uzodinma ya yi ikirari?
Share
Latest News
BLIND SPOT: Nigeria’s shortcomings in the age of AI scams
The rise of deepfakes and the fight for digital truth
DISINFO ALERT: Health ministry debunks AI video claiming free nationwide diabetes treatment
Video wey show as ‘security operatives’ dey break into apartment no be from south-east
Íhé ńgósị́ ébé ńdị́ ǹché nà-ákpáká ụ́lọ̀ ésiteghị nà south-east
Ìṣẹ̀lẹ tí àwọn ‘òṣìṣẹ́ elétò ààbò’ fẹ́ fipá wọ ibùgbé kan kò ṣẹlẹ̀ ní gúúsù ilà oòrùn Nàìjíríà
Bidiyon da ake dangantawa da ‘jami’an tsaro’ da suka kutsa cikin gida ba daga kudu maso gabas ba ne
FACT CHECK: Video attributed to ‘security operatives’ breaking into apartment isn’t from south-east
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

‘Shin ‘yan jam’iyyar APC ne kadai aka kai hari an Imo kamar yadda Uzodinma ya yi ikirari?

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published January 11, 2023 4 Min Read
Share

Hope Uzodimma, gwamnan jihar Imo, ya ce ‘yan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da mutanen da ke kusa da gwamnatinsa ne kadai ke fama da hare-haren rashin tsaro a jihar.

Uzodimma ya kuma yi zargin cewa ‘yan siyasa ne ke haddasa rashin tsaro a jihar.

Gwamnan Imo ya yi wannan ikirarin ne a ranar Alhamis yayin wani shiri a gidan Talabijin na Channels.

Events of the past have shown clearly that politicians are the ones behind the insecurity in Imo State.

– Sen. Hope Uzodimma, Governor of Imo State.#CTVTweets pic.twitter.com/hW2Pc2vm14

— Channels Television (@channelstv) January 5, 2023

“A yau, a tattaunawar da na yi da masu ruwa da tsaki a jihar Imo, na bayyana karara cewa abubuwan da suka faru a baya sun nuna karara cewa wadanda ke haddasa rashin tsaro a jihar Imo ‘yan siyasa ne, kuma wannan rashin tsaro na siyasa ne.” Inji Uzodimma.

“Misali, a waccan jawabin da na yi, na fito da matsaya a fili cewa duk mutanen da aka kai wa hari a Jihar Imo, da gidajen da aka kona, ‘yan APC ne kuma na kusa da gwamnati na.

“Idan ka duba, babu wani dan wata jam’iyyar siyasa da aka kai wa hari a jihar Imo; babu wani dan jam’iyyar adawa da aka kona gidansa, kuma hakan ya ci gaba da faruwa.

“Kawai ka ambaci na tsohon gwamna Ikedi Ohakin, kwanaki uku bayan ya kira liyafar cin abinci na musamman na masu ruwa da tsaki na Imo, ya kuma karfafa masu gwiwa da su marawa gwamnatin APC baya, bayan kwana biyu, an kai masa hari tare da kashe bayanan tsaronsa.

Kun ambaci tsohon gwamna Ikedi Ohakin. Bayan kwanaki uku da ya kira liyafar cin abinci na musamman ga masu ruwa da tsaki na jihar Imo tare da karfafa masu gwiwa da su marawa gwamnatin APC baya, bayan kwana biyu aka kai masa hari kuma aka kashe masu tsaron shi.

“Don haka, na gabatar da wannan al’amari ga mutanen Imo, an kama wasu – wasu manya daga cikin masu laifin.

“Don haka na kalubalanci jami’an tsaro a jihar Imo da su gaggauta bayyana rahotan wannan bincike da kuma wadanda ke da hannu wajen kashe-kashen a jihar ta Imo.

“Kuma za su yi haka kawai. Ba zan yi riya game da hakan ba. Ba zan yi siyasa da tsaron jihar Imo ba.”

TABBATARWA

A makonnin baya-bayan nan ne dai jaridar TheCable jerin hare-hare kan kadarorin kuma ‘yan siyasa da ‘yan bindiga suka yi a jihar Imo.

A kwanakin baya ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari kan ayarin motocin Ikedi Ohakim, tsohon gwamnan Imo, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar jami’an ‘yan sanda hudu.

A watan Disambar 2022, wasu ‘yan bindiga sun bankawa wata kotun majistare dake karamar hukumar Owerri da wata babbar kotu dake karamar hukumar Orlu ta jihar Imo wuta cikin sa’o’i 24.

Haka kuma a watan Disambar 2022, wasu ‘yan bindiga sun kashe Christopher Eleghu, dan takarar jam’iyyar Labour Party (LP) a mazabar Onuimo a majalisar dokokin jihar Imo.

A ranar 12 ga watan Disamba ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari a ofishin hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) da ke Owerri, babban birnin jihar Imo.

HUKUNCI

Maganar da Uzodimma ya yi na cewa ‘yan jam’iyyar APC da makusantan gwamnatin sa ne kawai aka kaiwa hari ba daidai ba ne.

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari tare da kashe dan takarar majalisar wakilai na jam’iyyar Labour a mazabar Onuimo, Christopher Eleghu a gidansa da ke Imo.

TAGGED: APC, attack, Fact Check, Imo State, Insecurity, Uzodinma

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi January 11, 2023 January 11, 2023
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

BLIND SPOT: Nigeria’s shortcomings in the age of AI scams

It sounded exactly like her, but it was not. Adeola Fayehun was thousands of miles…

August 12, 2025

The rise of deepfakes and the fight for digital truth

BY PRUDENCE OKEOGHENE EMUDIANUGHE On May 30, 2025, a 49-minute video surfaced on a YouTube…

August 12, 2025

DISINFO ALERT: Health ministry debunks AI video claiming free nationwide diabetes treatment

The ministry of health and social welfare has dismissed a viral claim alleging the launch…

August 12, 2025

Video wey show as ‘security operatives’ dey break into apartment no be from south-east

One Facebook user don claim sey video wey show as hooded armed security operatives dey…

August 7, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Video wey show as ‘security operatives’ dey break into apartment no be from south-east

One Facebook user don claim sey video wey show as hooded armed security operatives dey break into residential apartment hapun…

CHECK AM FOR WAZOBIA
August 7, 2025

Íhé ńgósị́ ébé ńdị́ ǹché nà-ákpáká ụ́lọ̀ ésiteghị nà south-east

Ótù onye na Facebook ekwuola na ihe ngosị ebe mmadụ na-agbaka ụlọ obibi mmadụ mere na south-east. N'ụbọchị iri abụọ…

CHECK AM FOR WAZOBIA
August 7, 2025

Ìṣẹ̀lẹ tí àwọn ‘òṣìṣẹ́ elétò ààbò’ fẹ́ fipá wọ ibùgbé kan kò ṣẹlẹ̀ ní gúúsù ilà oòrùn Nàìjíríà

Ẹni kan tí ó ń lo Facebook, ohun ìgbàlódé íbaraẹnisọrẹ lórí ayélujára sọ pé fídíò tí ó se afihan àwọn…

CHECK AM FOR WAZOBIA
August 7, 2025

Bidiyon da ake dangantawa da ‘jami’an tsaro’ da suka kutsa cikin gida ba daga kudu maso gabas ba ne

Wani ma’abocin amfani da shafin Facebook ya yi ikirarin cewa wani faifan bidiyo da ke nuna jami’an tsaro dauke da…

CHECK AM FOR WAZOBIA
August 7, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?