TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: Shin CBN ya gabatar da N5,000, N2,000 kamar yadda aka yi ikirari a wani bidiyo?
Share
Latest News
FACT CHECK: Is Nigeria 4th fastest-growing economy in the world in 2025?
FACT CHECK: How true are Obi’s claims about poverty rate in Nigeria, China and Indonesia?
FACT CHECK: No, Finnish court didn’t approve Simon Ekpa’s extradition to Nigeria
FACT CHECK: Is Cardinal Arinze eligible to be elected as the next Pope?
Rárá, Jonathan kò sọ pé Tinubu yóò se àṣeyọrí nínú ètò ìdìbò fún Ipò Ààrẹ ní ọdún 2027
A’a, Jonathan bai yi hasashen nasarar Tinubu a zaben shugaban kasa na 2027 ba
No, Jonathan no predict Tinubu victory for 2027 presidential election
Ḿbà, Jonathan ágbaghị àmà na Tinubu gà-èmérí ńtùlíáka ónyé ísíàlà ǹkè áfọ̀ 2027
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

Shin CBN ya gabatar da N5,000, N2,000 kamar yadda aka yi ikirari a wani bidiyo?

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published November 19, 2022 6 Min Read
Share

Wani bidiyo da ke nuna N5,000 da N2,000 ya kasance yana yawo a yanar gizo.

A cikin faifan bidiyon, wanda aka yada a shafin Twitter a ranar 27 ga Oktoba, wata mata ta nuna tarin kudi N5,000 da N2,000.

I hope this is a joke . pic.twitter.com/p8GM6YS1pA

— Dr Penking™🇳🇬🇦🇺 (@drpenking) October 27, 2022

Matar tace wani mahaukaci ne ya zo ya ajiye shi a reshen bankin da take aiki.

“Ina fatan wannan wasa ne,” inji rubutun da akayi a kasan bidiyon wanda mutane sama da 33,000 suka kalla, mutane 1,028 sun danna like da kuma retweets 367.

An kuma yada ta a Instagram da kuma asusu da yawa a Facebook, inda ‘yan Najeriya da dama da ba a san ko su wanene ba suka nuna kaduwa da wannan ci gaba.

A ranar 26 ga watan Oktoba, Godwin Emefiele, gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), ya ce babban bankin ya sanar da sake fasalin wasu takardun kudi na Naira.

Emefiele ya ce sabon tsarin wanda ya hada da N200, N500 da N1000 zai fara aiki daga tsakiyar watan Disamba na 2022.

Gwanman CBN ya kare da cewa chanjin fasalin kudin sakamakon kalubalen da kasar ke fuskanta ne a bangaren kula da kudi dake kokarin bata mutuncin CBN da kasar.

Tabbatarwa

TheCable ta saka bidiyon a Invid, wani na’ura dake duba ingancin bidiyo, domin gudanar da bincike a bidiyon. Binciken ya nuna bidiyon ya dade yana yawo a Facebook da YouTube tun 2020.

Daga abun da ake gani, a gefe daya na N5000 din ana ganin hoton wani mutun sanye da hula, a dayan gefen kuma, hoton mata ne guda uku dake kusa da juna.

Binciken da akayi a Google ya nuna cewa a Agustan 2012, CBN ta sanar da shirin buga kudin N5,000.

Sanusi Lamido, gwamnan CBN a lokacin yace fuskokin manyan mata uku yan Nijeriya za a saka a sabon kudin wadan da suka hada da Margaret Ekpo, yar siyasa da ta mutu; Hajia Gambo Sawaba, yar siyasa da ta mutu, da Funmilayo Kuti, yar siyasa da ta mutu.

Lamido yace yin kudin N5000 zai kara wa kudin kasar inganci da kuma rage yawan kudin da ake biya wurin buga kudin.

Sai dai, biyo bayan maganar sa, aka yi ta sukar buga sabon kudi. Kungiyar ICAN tace idan CBN ta buga kudin N5000 zai rage wa naira daraja.

Gwamnatin Nijeriya, da farko ta amince, amma daga bisani ta dakatar da yin kudin N5000 domin “ta ba CBN lokaci ta sake yin bincike da nazari akan batun.

A ranar 31 ga watan Mayun 2020, CBN a shafin ta na Twitter, tayi kira ga yan Nijeriya da suyi watsi da hotuna da bidiyo na bogi da ke yawo a lokacin.

Sanusi Lamido, gwamnan babban bankin na CBN, ya ce fuskokin wasu fitattun ‘yan gwagwarmaya mata uku na Najeriya da za a yi amfani da su a wannan sabuwar takardar sun hada da Margaret Ekpo, tsohuwar ‘yar siyasa kuma mai wayar da kan jama’a; Hajiya Gambo Sawaba, tsohuwar ‘yar siyasa ce kuma ‘yar gwagwarmaya, da Funmilayo Kuti, marigayiya ‘yar siyasa kuma ‘yar fafutukar kare hakkin mata.

Lamido yace yin kudin N5000 zai kara wa kudin kasar inganci da kuma rage yawan kudin da ake biya wurin buga kudin.

Duk da haka, ci gaban ya gamu da koma baya da suka da yawa. Cibiyar da ke kula da Akantoci ta Najeriya (ICAN) ta ce bullo da takardar kudi na N5000 da CBN ta yi na iya kara janyo faduwar darajar Naira.

Gwamnatin Najeriya, duk da amincewar da ta samu a baya, ta dakatar da gabatar da N5000 don “baiwa CBN damar yin karin haske kan lamarin”.

Haka kuma, CBN ta shafinta na Twitter a ranar 31 ga Mayu, 2020, ta bukaci ‘yan Najeriya da su yi watsi da hotuna da bidiyoyin karya da ake yadawa a wancan lokacin.

“Bidiyo da hotunan da aka ce ana yadawa na N2,000:00 da Naira 5,000:00 karya ne kuma na bogi. An shawarci jama’a da su yi watsi da irin wannan karyar, kuma su kai rahoton duk wanda aka samu da irin wadannan takardun ga jami’an tsaro,” CBN ta wallafa a shafinta na Twitter.

Videos and pictures of purported circulation of N2,000:00 and N5,000:00 banknotes are false and fake. Members of the public are advised to disregard such falsehood and to report anyone found in possession of such banknotes to the law enforcement agencies

— Central Bank of Nigeria (@cenbank) May 31, 2020

Ana raba tsohon bidiyon a dandamalin kafofin watsa labarun a cikin tsammanin tsakiyar watan Disamba 2022 da aka sanar kwanan wata don sakin kudin da aka sake fasalin.

A halin da ake ciki, CBN ya sanar da sake fasalin N200, N500, da N1000, babban bankin bai taba bayyana wani shiri na gabatar da takardun kudi na N2000 ko N5000 ba.

Hukunci

Bidiyon da ake yadawa na cewa gwamnatin tarayya na gabatar da N2,000 da N5,000 karya ne. Bidiyon kudin bogin yana ta yawo a yanar gizo tun 2020.

TAGGED: cbn, Godwin Emiefele, N2000, N5000, Naira redesign

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi November 19, 2022 November 19, 2022
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

FACT CHECK: Is Nigeria 4th fastest-growing economy in the world in 2025?

A viral post claims, based on International Monetary Fund (IMF) projections, that Nigeria ranks fourth…

May 9, 2025

FACT CHECK: How true are Obi’s claims about poverty rate in Nigeria, China and Indonesia?

Peter Obi, Labour Party (LP) presidential candidate in the 2023 elections, sparked a debate with…

May 5, 2025

FACT CHECK: No, Finnish court didn’t approve Simon Ekpa’s extradition to Nigeria

On Tuesday, some social media users and blog sites made a post claiming that a…

April 24, 2025

FACT CHECK: Is Cardinal Arinze eligible to be elected as the next Pope?

A social media user has claimed that Francis Arinze, a Roman Catholic cardinal, is the…

April 21, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Rárá, Jonathan kò sọ pé Tinubu yóò se àṣeyọrí nínú ètò ìdìbò fún Ipò Ààrẹ ní ọdún 2027

Ní ọjọ́ ajé, ọ̀rọ̀ kan to sọ pé Goodluck Jonathan, Ààrẹ orílẹ̀ èdè Nàìjíríà tẹ́lẹ̀ sọ pé Ààrẹ Bọla Tinubu…

CHECK AM FOR WAZOBIA
April 20, 2025

A’a, Jonathan bai yi hasashen nasarar Tinubu a zaben shugaban kasa na 2027 ba

A ranar Talata ne wani rahoto da ke ikirarin cewa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya yi hasashen nasarar Shugaba…

CHECK AM FOR WAZOBIA
April 20, 2025

No, Jonathan no predict Tinubu victory for 2027 presidential election

On Tuesday, one report wey claim sey former President Goodluck Jonathan predict President Bola Tinubu victory for di 2027 presidential…

CHECK AM FOR WAZOBIA
April 20, 2025

Ḿbà, Jonathan ágbaghị àmà na Tinubu gà-èmérí ńtùlíáka ónyé ísíàlà ǹkè áfọ̀ 2027

N’ubọchị Tuesde, ozi na-ekwu na onye bụburu onye isiala Naijiria, bụ Goodluck Jonathan, gbara àmà na onyeisiala Bola Tinubu ga-emeri…

CHECK AM FOR WAZOBIA
April 19, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?