TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: Shin Borno girman daya da UK da Sweden kamar yadda Osinbajo yayi ikirari?
Share
Latest News
MISINFO ALERT: Video of man shot by operative over ‘N5k bribe’ is from 2019, says customs
How to protect yourself from misinformation, disinformation in the AI age
FACT CHECK: Did Ibrahim Traore cancel Burna Boy’s proposed Burkina Faso concert?
CableCheck wins IFCN global fact check fund
Íhé ńgósị́ ébé Peter Obi sékpù àlà n’íhú Tinubu bụ̀ ǹkè é jìrì AI nwóghàrị̀á
Hoton Peter Obi ya durkusa ma Tinubu a Rome na hadi ne
Foto wey show as Peter Obi dey kneel down for Tinubu inside Vatican na photoshop
Peter Obi kò kúnlẹ̀ fún Tinubu ní Rome
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

Shin Borno girman daya da UK da Sweden kamar yadda Osinbajo yayi ikirari?

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published September 12, 2022 5 Min Read
Share

Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana cewa jihar Borno tana da girman kasar Ingila (Birtaniya) da Sweden a hade ko kuma Burtaniya da Denmark.

Laolu Akande, mai magana da yawun Osinbajo, a wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana cewa mataimakin shugaban kasar ya tattauna da kungiyar daliban makarantar kasuwanci ta Harvard da suka ziyarce shi a fadar shugaban kasa a ranar Lahadi, 28 ga watan Agusta.

Yayin da yake zantawa da daliban da suka yi Ziaran Bude-Ido Afirka, Osinbajo ya ce domin kasashen duniya su kara fahimtar girma da sarkakiyar kalubalen tattalin arziki da tsaro da Najeriya ke fuskanta, yana da kyau a yi la’akari da girman kasar.

“Na farko, akwai bukatar a yaba da girman kasar, wanda ke da matukar muhimmanci wajen fahimtar mene ne batutuwa.

“Misali, jihar Borno, girman ta kusan daya ne da gabadaya UK a hade da Sweden ko Denmark.

Saboda haka, idan akayi rahoto akan cewa akwai tashin hankali a Nijeriya, baze wuce a wani bangare daya na kasar ba, sannan mutane da yawa dake Abuja da Legas kila a shafun sada zumunta zasu ji, irin haka ne girman kasar nan.

“Idan ana maganan girman tattalin arziki, ana yawan hada mu da kananan kasashen Afurka, amma akwai jihohi guda 10 a Nijeriya da suka fi sauran kasashen girman GDP, babban kasuwa ne da za awa hari.”

Jihar Borno girman ta daya da gabadaya UK da Sweden ko Uk da Denmark idan aka hada su?

Labarin an buga shi a kafafen yada labarai daban-daban.

Tabbatarwa

TheCable ta duba griman jihar Borno, jihar dake Arewa maso gabashin kasar nan anyi ta ne a wata Febrairo 1976. An kara rabata a 1991, sanda aka fidda jihar Yobe daga cikin ta.

Jihar Borno, wadda akafi sanin ta da taken ‘Home of peace’, daga yammacin da jihar Yobe ce. Jihar Borno ta kuma hada iyaka da kasar Niger daga Arewacin ta, da kuma Chad daga Arewa maso yamma sannan daga gabas din ta kuma kasar Kamaru.

Ainihin shafin gwamnatin jihar Borno yace gaba daya girma da fadin jihar shine 61,435sqkm, inda ta zama itace jiha ta biyu a girma bayan jihar Niger.

A bayanan da ofishin kididdiga na kasa (NBS) da hukumar kula da yawan jama’a ta kasa (NPC) na shekarar 2019 ya nuna cewa yawan mutanen dake jihar Borno sunkai mutane miliyan 5.7

United Kingdom ta hada da gabadaya Birtaniya, wanda ya kunshi Ingila, Wales da Scotland-tare da bangaren arewancin tsibirin Ireland.

Bayanan bankin duniya na 2021, ya nuna cewa girman United Kingdom yakai 241,930km2.

Ofishin kididdiga na UK, babban ofishi mai zaman kanta dake fidda sahihan kididdiga tace yawan mutanen dake UK mutane miliyan 67 ne.

Sweden ta na kan Scandinavian peninsula a arewacin nahiyar Turai. Babban birnin kasar Stockholm ne tun shekarar 1523. Sweden ce tafi kwashe girman Scandinavian Peninsula, wanda ita da Norway ke da iyaka.

Duka da kasar tana da tarihin shafe shekaru 1000 tana zaman kanta, fadin yanki bai chanza ba sai a shekarar 1809.

Bayanan bankin duniya na 2021 yana cewa girma da fadin kasar Sweden 407,310km2 sannan mutanen kasar miliyan 10.4 ne.

Denmark ita tana tsibirin Jutland, wanda ya miki har ta arewacin sa har zuwa tsakiyan nahiyar Turai ta yamma. Jutland ya kwashe kashi biyu cikin uku na girman kasar.

A shekarar 2021, bankin duniya ta bayyana girman Denmark a matsayin 40,000km2 da mutane yawan miliyan 5.8.

Jihar Borno, a girma tafi kasar Denmark, sannan yawan mutanen jihar kusan daya ne da yawan mutanen dake Denmark, amma akwai banbancin girma da yawan mutane tsakanin jihar Borno da Sweden da kuma United Kingdom.

Binciken da TheCable tayi ya nuna cewa girma da yawan mutane na United Kingdom kadai yafi na jihar Borno da nisa, balle a hada Uk da Sweden ko Denmark.

Borno United Kingdom  Sweden Denmark United Kingdom + Sweden United Kingdom + Denmark
Landmass (km²) 61,435 241,930  407,310  40,000  649,240  281,930
Population 5,751,590 67,081,000 10,415,811 5,856,733 77,496,811 72,937,733

Hukunci

Maganan mataimakin shugaban kasa Osinbajo na jihar Borno girman ta daya da UK da Sweden a hade ko UK da Denmark a hade ba gaskiya bane, an zuzuta shi ne.

TAGGED: borno state, Check Am For Wazobia, Denmark, Sweden, United Kingdom, Yemi Osinbajo.

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi September 12, 2022 September 12, 2022
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

MISINFO ALERT: Video of man shot by operative over ‘N5k bribe’ is from 2019, says customs

The Nigeria Customs Service (NCS) has reacted to a viral video showing its operatives implicated…

June 5, 2025

How to protect yourself from misinformation, disinformation in the AI age

The internet has made life somewhat easier, right? You want to read the news and…

June 4, 2025

FACT CHECK: Did Ibrahim Traore cancel Burna Boy’s proposed Burkina Faso concert?

There are reports that Ibrahim Traore, Burkina Faso’s military leader, has cancelled Afrofusion star Burna…

June 3, 2025

CableCheck wins IFCN global fact check fund

CableCheck, the fact-checking initiative of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), has been awarded the…

May 30, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Íhé ńgósị́ ébé Peter Obi sékpù àlà n’íhú Tinubu bụ̀ ǹkè é jìrì AI nwóghàrị̀á

Ótù ihe ngosị nke a na-ekesa na soshal midia na-egosị ebe Peter Obi, onye jiri Labour Party zọ ọkwa onye…

CHECK AM FOR WAZOBIA
May 24, 2025

Hoton Peter Obi ya durkusa ma Tinubu a Rome na hadi ne

Wani hoton da ya yi zagayen a shafukan sada zumunta ya nuna Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar…

CHECK AM FOR WAZOBIA
May 24, 2025

Foto wey show as Peter Obi dey kneel down for Tinubu inside Vatican na photoshop

One foto wey don waka for social media show as Peter Obi, presidential candidate of di Labour Party (LP) for…

CHECK AM FOR WAZOBIA
May 24, 2025

Peter Obi kò kúnlẹ̀ fún Tinubu ní Rome

Àwọn ènìyàn ti ń pín àwòrán kan kiri lórí ohun ìgbàlódé ibaraẹnise orí ayélujára, tí ó se àfihàn Peter Obi,…

CHECK AM FOR WAZOBIA
May 24, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?