TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: Shin Borno girman daya da UK da Sweden kamar yadda Osinbajo yayi ikirari?
Share
Latest News
FACT CHECK: Video showing ‘bridge collapsing in Nasarawa’ is AI-generated
MISINFO ALERT: Viral video of ‘foreign arms dealer’ in Zamfara is from 2021, says army
Ókwú Badenoch nà ụ́mụ̀ yá ápụ̀ghị̀ ínwétá íkíké ị́bụ ńdị́ Naijiria bụ̀ àsị́
Kemi Badenoch claim sey her children no fit get Nigerian citizenship but she no tok true
Irọ́ ni Kemi Badenoch pa pé òfin kò fààyè gba àwọn ọmọ òhun láti di ọmọ Nàìjíríà
Maganar Kemi Badenoch na cewa ‘ya’yanta ba za su iya samun shaidar zama dan Najeriya ba karya ne
FACT CHECK: Kemi Badenoch’s claim that her children can’t get Nigerian citizenship is false
Naijiria ọ̀ kàgbùrù ńkwékọ́rị́tá àzụ́máhị́á àkụ̀ ọ̀nàtàràchí yá nà US nwèrè n’íhì ḿmáchí visa?
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

Shin Borno girman daya da UK da Sweden kamar yadda Osinbajo yayi ikirari?

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published September 12, 2022 5 Min Read
Share

Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana cewa jihar Borno tana da girman kasar Ingila (Birtaniya) da Sweden a hade ko kuma Burtaniya da Denmark.

Laolu Akande, mai magana da yawun Osinbajo, a wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana cewa mataimakin shugaban kasar ya tattauna da kungiyar daliban makarantar kasuwanci ta Harvard da suka ziyarce shi a fadar shugaban kasa a ranar Lahadi, 28 ga watan Agusta.

Yayin da yake zantawa da daliban da suka yi Ziaran Bude-Ido Afirka, Osinbajo ya ce domin kasashen duniya su kara fahimtar girma da sarkakiyar kalubalen tattalin arziki da tsaro da Najeriya ke fuskanta, yana da kyau a yi la’akari da girman kasar.

“Na farko, akwai bukatar a yaba da girman kasar, wanda ke da matukar muhimmanci wajen fahimtar mene ne batutuwa.

“Misali, jihar Borno, girman ta kusan daya ne da gabadaya UK a hade da Sweden ko Denmark.

Saboda haka, idan akayi rahoto akan cewa akwai tashin hankali a Nijeriya, baze wuce a wani bangare daya na kasar ba, sannan mutane da yawa dake Abuja da Legas kila a shafun sada zumunta zasu ji, irin haka ne girman kasar nan.

“Idan ana maganan girman tattalin arziki, ana yawan hada mu da kananan kasashen Afurka, amma akwai jihohi guda 10 a Nijeriya da suka fi sauran kasashen girman GDP, babban kasuwa ne da za awa hari.”

Jihar Borno girman ta daya da gabadaya UK da Sweden ko Uk da Denmark idan aka hada su?

Labarin an buga shi a kafafen yada labarai daban-daban.

Tabbatarwa

TheCable ta duba griman jihar Borno, jihar dake Arewa maso gabashin kasar nan anyi ta ne a wata Febrairo 1976. An kara rabata a 1991, sanda aka fidda jihar Yobe daga cikin ta.

Jihar Borno, wadda akafi sanin ta da taken ‘Home of peace’, daga yammacin da jihar Yobe ce. Jihar Borno ta kuma hada iyaka da kasar Niger daga Arewacin ta, da kuma Chad daga Arewa maso yamma sannan daga gabas din ta kuma kasar Kamaru.

Ainihin shafin gwamnatin jihar Borno yace gaba daya girma da fadin jihar shine 61,435sqkm, inda ta zama itace jiha ta biyu a girma bayan jihar Niger.

A bayanan da ofishin kididdiga na kasa (NBS) da hukumar kula da yawan jama’a ta kasa (NPC) na shekarar 2019 ya nuna cewa yawan mutanen dake jihar Borno sunkai mutane miliyan 5.7

United Kingdom ta hada da gabadaya Birtaniya, wanda ya kunshi Ingila, Wales da Scotland-tare da bangaren arewancin tsibirin Ireland.

Bayanan bankin duniya na 2021, ya nuna cewa girman United Kingdom yakai 241,930km2.

Ofishin kididdiga na UK, babban ofishi mai zaman kanta dake fidda sahihan kididdiga tace yawan mutanen dake UK mutane miliyan 67 ne.

Sweden ta na kan Scandinavian peninsula a arewacin nahiyar Turai. Babban birnin kasar Stockholm ne tun shekarar 1523. Sweden ce tafi kwashe girman Scandinavian Peninsula, wanda ita da Norway ke da iyaka.

Duka da kasar tana da tarihin shafe shekaru 1000 tana zaman kanta, fadin yanki bai chanza ba sai a shekarar 1809.

Bayanan bankin duniya na 2021 yana cewa girma da fadin kasar Sweden 407,310km2 sannan mutanen kasar miliyan 10.4 ne.

Denmark ita tana tsibirin Jutland, wanda ya miki har ta arewacin sa har zuwa tsakiyan nahiyar Turai ta yamma. Jutland ya kwashe kashi biyu cikin uku na girman kasar.

A shekarar 2021, bankin duniya ta bayyana girman Denmark a matsayin 40,000km2 da mutane yawan miliyan 5.8.

Jihar Borno, a girma tafi kasar Denmark, sannan yawan mutanen jihar kusan daya ne da yawan mutanen dake Denmark, amma akwai banbancin girma da yawan mutane tsakanin jihar Borno da Sweden da kuma United Kingdom.

Binciken da TheCable tayi ya nuna cewa girma da yawan mutane na United Kingdom kadai yafi na jihar Borno da nisa, balle a hada Uk da Sweden ko Denmark.

Borno United Kingdom  Sweden Denmark United Kingdom + Sweden United Kingdom + Denmark
Landmass (km²) 61,435 241,930  407,310  40,000  649,240  281,930
Population 5,751,590 67,081,000 10,415,811 5,856,733 77,496,811 72,937,733

Hukunci

Maganan mataimakin shugaban kasa Osinbajo na jihar Borno girman ta daya da UK da Sweden a hade ko UK da Denmark a hade ba gaskiya bane, an zuzuta shi ne.

TAGGED: borno state, Check Am For Wazobia, Denmark, Sweden, United Kingdom, Yemi Osinbajo.

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi September 12, 2022 September 12, 2022
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

FACT CHECK: Video showing ‘bridge collapsing in Nasarawa’ is AI-generated

A video showing a bridge collapse incident is circulating across social media platforms, especially on…

July 24, 2025

MISINFO ALERT: Viral video of ‘foreign arms dealer’ in Zamfara is from 2021, says army

The Nigerian Army says a viral video claiming the arrest of a foreign arms dealer…

July 24, 2025

Ókwú Badenoch nà ụ́mụ̀ yá ápụ̀ghị̀ ínwétá íkíké ị́bụ ńdị́ Naijiria bụ̀ àsị́

Kemi Badenoch, onye ndú òtù Conservative Party nke obodo United Kingdom, ekwuola na ọ gaghị…

July 22, 2025

Kemi Badenoch claim sey her children no fit get Nigerian citizenship but she no tok true

Kemi Badenoch, leader of di United Kingdom Conservative Party, claim sey she no fit pass…

July 22, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Ókwú Badenoch nà ụ́mụ̀ yá ápụ̀ghị̀ ínwétá íkíké ị́bụ ńdị́ Naijiria bụ̀ àsị́

Kemi Badenoch, onye ndú òtù Conservative Party nke obodo United Kingdom, ekwuola na ọ gaghị enyenwu ụmụ ya ikike ịbụ…

CHECK AM FOR WAZOBIA
July 22, 2025

Kemi Badenoch claim sey her children no fit get Nigerian citizenship but she no tok true

Kemi Badenoch, leader of di United Kingdom Conservative Party, claim sey she no fit pass her right of Nigerian citizenship…

CHECK AM FOR WAZOBIA
July 22, 2025

Irọ́ ni Kemi Badenoch pa pé òfin kò fààyè gba àwọn ọmọ òhun láti di ọmọ Nàìjíríà

Kemi Badenoch, arábìnrin tó jẹ́ olórí ẹgbẹ́ òsèlú alátakò tí wọ́n ń pè ní Conservative Party ní orílẹ̀ èdè United…

CHECK AM FOR WAZOBIA
July 22, 2025

Maganar Kemi Badenoch na cewa ‘ya’yanta ba za su iya samun shaidar zama dan Najeriya ba karya ne

Kemi Badenoch, shugabar jam'iyyar masu ra'ayin rikau ta Burtaniya, ta yi ikirarin cewa ba za ta iya mika hakkinta na…

CHECK AM FOR WAZOBIA
July 22, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?