TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: Shin bidiyon rawa na Aregbesola yana da nasaba da soke takarar gwamna Oyetola?
Share
Latest News
FACT CHECK: Did Nigeria halt ‘mineral deal’ with US after visa restrictions?
FACT CHECK: Viral image depicting ‘Obasanjo prostrating for Ladoja’ photoshopped
Wike tụ̀rụ̀ àsị́. Peter Obi mèrè ńtụ̀líáká ọ̀chị́chị́ ḿpághárá m̀gbè ọ́ bụ̀ gọ́vánọ̀ Anambra
Irọ́ ni Wike pa. Peter Obi ṣètò ìdìbò ìjọba ìbílẹ̀ nígbà tí ó jẹ́ gómìnà Ìpínlẹ̀ Anambra
Wike yayi kuskure. Peter Obi ya gudanar da zaben LG a matsayin gwamnan Anambra
Wike make mistake. Peter Obi conduct LG election as Anambra governor
Video wey show as Thomas Partey dey blame ‘rape’ case on racism na fake
Bidiyon da ke nuna Partey yana zargin shari’ar ‘fyade’ akan wariyar launin fata da aka gyara ta hanyar lambobi
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

Shin bidiyon rawa na Aregbesola yana da nasaba da soke takarar gwamna Oyetola?

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published October 10, 2022 3 Min Read
Share

Wani faifan bidiyo da ke nuna Rauf Aregbesola, ministan harkokin cikin gida kuma tsohon gwamnan jihar Osun yana rawa a yanar gizo.

A shafin Twitter, an yada hoton bidiyon tare da ikirarin cewa ministan na rawa ne domin murnar soke zaben gwamnan Osun, Gboyega Oyetola a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zaben da aka gudanar a jihar.

Wani mai shafi a Twitter, @IfedolapoOsun ne ya wallafa wannan sakon a ranar Juma’a, 30 ga watan Satumba, a ranar da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta soke zaben Gboyega Oyetola da mataimakinsa, Benedict Alabi, a matsayin ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar APC.

Aregbesola Today after Court Nullified Gboyega Oyetola's candidacy 🤣🤣 pic.twitter.com/2fEi8tbS1P

— Governor Ifedolapo Osun (@IfedolapoOsun) September 30, 2022

Bidiyon ya tattara kan 23,400 views, 879 likes da 352 retweets.

An raba bidiyon tare da taken “Aregbesola A Yau bayan Kotu ta soke takarar Gboyega Oyetola”.

Shafin Twittern da aka fara tura bidiyon na dauke ne da hoton Ademola Adeleke. Hakan ya ja hankalin wasu masu amfani da Twitter sukayi tunanin Ademola Adeleke, gwamna me jiran gado na Osun, ne ya tura bidiyon.

Abun da ya faru a baya

Alkalin kotun Emeka Nwite, ya yanke hukuncin ne a wata kara mai lamba FHC/ABJ/CS/468/2022 da jam’iyyar PDP ta shigar.

A karar, Mai Mala Buni, tsohon shugaban riko na jam’iyyar APC, da wasu hudu sun kasance wadanda ake tuhuma.

Nwite, a hukuncin da ya yanke, ya ce nadin Oyetola da mataimakinsa ba bisa ka’ida ba ne, kuma ya sabawa kundin tsarin mulkin kasa, domin Buni, wanda ya mika sunayensu ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ya saba tanadin sashe na 183 na kundin tsarin mulki da sashe na 82(3) ) na dokar zabe 2022.

Tabbatarwa

Binciken da TheCable ta yi ya nuna cewa wani ma’abocin Facebook, Ajiboye Maroof Akinlabi ne ya saka bidiyon a ranar Litinin, 26 ga Satumba, tare da bayanin: “Ministan harkokin cikin gida Ogbeni RAUF AREGBESOLA yana murnar cika shekaru 62 da haihuwar matarsa Ìyáàfin Sherifat Aregbesola”.

Kikiowo Ileowo, mataimaki na musamman ga Rauf Aregbesola, a lokacin da jaridar TheCable ta tuntubi ta, ya ce, “bikin ba shi da alaka da hukuncin da kotu ta yanke na soke Oyetola”, ya kara da cewa an dauki hoton bidiyon ne kwanaki da suka gabata a yayin bikin zagayowar ranar haihuwar matar Aregbesola.

Hukunci

Bidiyon raye-rayen da ake dangantawa da Aregbesola na murnar soke Oyetola na yaudara ne. An buga wani sigar farko a ranar Litinin, 23 ga Satumba, yayin da kotu ta yanke hukuncin a ranar Juma’a, 28 ga Satumba.

TAGGED: Aregbesola, Oyetola

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi October 10, 2022 October 10, 2022
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

FACT CHECK: Did Nigeria halt ‘mineral deal’ with US after visa restrictions?

A Facebook user has claimed that Nigeria retaliated against the recent United States visa restrictions…

July 15, 2025

FACT CHECK: Viral image depicting ‘Obasanjo prostrating for Ladoja’ photoshopped

An image showing a person prostrating for Rashidi Ladoja, the Olubadan-in-waiting and former governor of…

July 11, 2025

Wike tụ̀rụ̀ àsị́. Peter Obi mèrè ńtụ̀líáká ọ̀chị́chị́ ḿpághárá m̀gbè ọ́ bụ̀ gọ́vánọ̀ Anambra

Nyesom Wike, onye minista nke isi obodo Naijiria bụ FCT, kwuru na Peter Obi, onye…

July 11, 2025

Irọ́ ni Wike pa. Peter Obi ṣètò ìdìbò ìjọba ìbílẹ̀ nígbà tí ó jẹ́ gómìnà Ìpínlẹ̀ Anambra

Nyesom Wike, minisita fún Federal Capital Territory (FCT), Abuja, olú ìlú orílẹ̀ èdè Nàìjíríà, sọ…

July 11, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Wike tụ̀rụ̀ àsị́. Peter Obi mèrè ńtụ̀líáká ọ̀chị́chị́ ḿpághárá m̀gbè ọ́ bụ̀ gọ́vánọ̀ Anambra

Nyesom Wike, onye minista nke isi obodo Naijiria bụ FCT, kwuru na Peter Obi, onye bụ buru gọvanọ Anambra steetị…

CHECK AM FOR WAZOBIA
July 11, 2025

Irọ́ ni Wike pa. Peter Obi ṣètò ìdìbò ìjọba ìbílẹ̀ nígbà tí ó jẹ́ gómìnà Ìpínlẹ̀ Anambra

Nyesom Wike, minisita fún Federal Capital Territory (FCT), Abuja, olú ìlú orílẹ̀ èdè Nàìjíríà, sọ pé Peter Obi, ẹni tí…

CHECK AM FOR WAZOBIA
July 11, 2025

Wike yayi kuskure. Peter Obi ya gudanar da zaben LG a matsayin gwamnan Anambra

Nyesom Wike, ministan babban birnin tarayya Abuja, ya ce Peter Obi, tsohon gwamnan Anambra kuma dan takarar shugaban kasa na…

CHECK AM FOR WAZOBIA
July 11, 2025

Wike make mistake. Peter Obi conduct LG election as Anambra governor

Nyesom Wike, minister of di Federal Capital Territory (FCT), tok sey Peter Obi, forma govnor of Anambra and 2023 Labour…

CHECK AM FOR WAZOBIA
July 11, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?