TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: Bidiyon shugaban kasar Zambiya ya na cewa ba zai tsaya takara ba na bogi ne
Share
Latest News
Seven ways to detect an AI-generated video
BLIND SPOT: Nigeria’s shortcomings in the age of AI scams
The rise of deepfakes and the fight for digital truth
DISINFO ALERT: Health ministry debunks AI video claiming free nationwide diabetes treatment
Video wey show as ‘security operatives’ dey break into apartment no be from south-east
Íhé ńgósị́ ébé ńdị́ ǹché nà-ákpáká ụ́lọ̀ ésiteghị nà south-east
Ìṣẹ̀lẹ tí àwọn ‘òṣìṣẹ́ elétò ààbò’ fẹ́ fipá wọ ibùgbé kan kò ṣẹlẹ̀ ní gúúsù ilà oòrùn Nàìjíríà
Bidiyon da ake dangantawa da ‘jami’an tsaro’ da suka kutsa cikin gida ba daga kudu maso gabas ba ne
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

Bidiyon shugaban kasar Zambiya ya na cewa ba zai tsaya takara ba na bogi ne

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published October 18, 2023 4 Min Read
Share

Jam’iyar United Party for National Development (UNDP) tayi watsi da wani bidiyo dake yawo dake nuna shugaba Hakainde Hichilema na Zambiya ya na cewa ba zai sake tsaya wa takara ba a zaben 2026.

A bidyon da ke ta yawo, ana iya ganin Hichilema sanye da kwat tare da tutar kasar Zambiya a bayan sa, ya na bayyana cewa ba zai nema yin tazarce ba a zaben da za a gudanar da kasar a 2026.

“Ina so shaida cewa ina sane da kalubalen da aka fuskanta a karkashin mulki na a matsayi na na shugaban wannan kasa mai albarka. Ina so na sanar da cewa ba zan yi takara ba a zaben da za ayi a 2026. A tunani na, wannan hukuncin dana dauka shine yafi don ci gaban kasar mu,” inji shi.

Hichilema yayi takaran shugaban kasa so biyar bai ci ba kafun yayi nasara daga baya a 2021.

A Zambiya, ana zaben shugaban kasa yayi shekaru 5 yana mulki kuma wa’adi biyu.

Idan aka ma bidiyo kallo na kusa-kusa, za aga motsin bakin da fitar maganar sa ba a tare suke tafiya ba, sannan bayan bidiyon yayi dishi-dishi. Ta nan za a gane anyi amfani da artificial intelligence (AI) a hada bidiyon.

Bidiyon na zuwa ne a lokacin da siyasar kasar Zambiya ke daukan zafi kafun zaben da za ayi a kasar a 2026.

Kamar yadda ake yi a sauran kasashe, idan lokacin zabe ya gabato, ana yawan yada bidiyoyi na karya don a yaudari mutane ko chanza musu tunani akan wadansu ‘yan takara.

A wata sanarwa da Batuke Imenda, sakatare janar na jam’iyar UPND mai mulki a Zambiya, ya zargi “yan bata gari” da “hadawa tare da yada bidiyoyi na karya da akayi amfani da muryar shugaban kasar da manufar a yaudari jama’a”.

“Mun fahimci wannan aiki ne na ‘yan adawa. Gaggawarsu har ya kai ga sun fara niyyan aikata laifi a kan shugaban da ‘yan kasa suka zaba,” inji sanarwar.

“Mun san wasu shuagabannin ‘yan adawa suna nan suna ta kokarin yin abubuwa da zasu janyo ma gwamnati mai mulki tarzoma.

“Mun san kuna neman mabiya ne kuma ku samu karbuwa amma zamu tunatar daku cewa doka makaho ne.

“Ba boyeyyen abu bane cewa wasu daga cikin ku suna abubuwan da suka sabawa doka don janyo hankalin jami’an tsaro. Sannan da zarar an kama ku don yin bincike, kune kuka fi kowa ihu.

“Jam’iyar tana so tayi kira ga duk wanda keda hannu a wannan bidiyon da ke ta yawo cewa zai kwashi kashin shi a hannu idan hukuma ta kama shi.”

Shugaban kasar bai ce komai ba har yanzu a game da bidiyon.

Saidai, rundunar ‘yan sandan kasar sunce sun fara bincike don gano wadanda suka hada bidiyon don a kama su kuma a hukuntasu.

TAGGED: AI-generated disinformation, Hakainde Hichilema, Hausa FactCheck, Zambia

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi October 18, 2023 October 18, 2023
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

Seven ways to detect an AI-generated video

A video announcing the launch of a free nationwide diabetes treatment recently went viral across Nigerian…

August 13, 2025

BLIND SPOT: Nigeria’s shortcomings in the age of AI scams

It sounded exactly like her, but it was not. Adeola Fayehun was thousands of miles…

August 12, 2025

The rise of deepfakes and the fight for digital truth

BY PRUDENCE OKEOGHENE EMUDIANUGHE On May 30, 2025, a 49-minute video surfaced on a YouTube…

August 12, 2025

DISINFO ALERT: Health ministry debunks AI video claiming free nationwide diabetes treatment

The ministry of health and social welfare has dismissed a viral claim alleging the launch…

August 12, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Video wey show as ‘security operatives’ dey break into apartment no be from south-east

One Facebook user don claim sey video wey show as hooded armed security operatives dey break into residential apartment hapun…

CHECK AM FOR WAZOBIA
August 7, 2025

Íhé ńgósị́ ébé ńdị́ ǹché nà-ákpáká ụ́lọ̀ ésiteghị nà south-east

Ótù onye na Facebook ekwuola na ihe ngosị ebe mmadụ na-agbaka ụlọ obibi mmadụ mere na south-east. N'ụbọchị iri abụọ…

CHECK AM FOR WAZOBIA
August 7, 2025

Ìṣẹ̀lẹ tí àwọn ‘òṣìṣẹ́ elétò ààbò’ fẹ́ fipá wọ ibùgbé kan kò ṣẹlẹ̀ ní gúúsù ilà oòrùn Nàìjíríà

Ẹni kan tí ó ń lo Facebook, ohun ìgbàlódé íbaraẹnisọrẹ lórí ayélujára sọ pé fídíò tí ó se afihan àwọn…

CHECK AM FOR WAZOBIA
August 7, 2025

Bidiyon da ake dangantawa da ‘jami’an tsaro’ da suka kutsa cikin gida ba daga kudu maso gabas ba ne

Wani ma’abocin amfani da shafin Facebook ya yi ikirarin cewa wani faifan bidiyo da ke nuna jami’an tsaro dauke da…

CHECK AM FOR WAZOBIA
August 7, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?