TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: Bidiyon ana yi wa gwamnan Kwara ihu daga shekarar 2018 ne
Share
Latest News
Rárá, Nàìjíríà kò fi àwọn ọmọ iṣẹ́ ológun rán sẹ sí Ísírẹ́lì láti dá rògbòdìyàn tó ń ṣẹlẹ̀ níbẹ̀ dúró
Ḿbà, Naijiria ézipụ̀ghị̀ ńdị́ ágha ńkwàdó ùdó nà òbòdò Isreal
No, Nigeria no send peace support mission go Israel
A’a, Najeriya ba ta tura tawagar taimakon zaman lafiya zuwa Isra’ila ba
Ǹjẹ́ Tinubu àti Alexander Zingman lọ sí ilé-ìwé kan náà? Èyí ni ohun tí a mọ̀
Tinubu nà Alexander Zingman ọ̀ gàrà ótù ụ́lọ̀ákwụ́kwọ́? Lèé íhé ányị́ mà
Tinubu go di same school wit Alexander Zingman? Na wetin we sabi be dis
Shin Tinubu ya halarci makaranta daya da Alexander Zingman? Ga abin da muka sani
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

Bidiyon ana yi wa gwamnan Kwara ihu daga shekarar 2018 ne

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published August 17, 2022 4 Min Read
Share

Wani bidiyon Abdulrahman Abdulrazaq, gwamnan jihar Kwara, dandazon jama’a nayi masa ihu ya bulla a yanar gizo.

A cikin dandazon jama’a ana jin mutane na kiran gwamnan ‘Ole’ da yaren yarbanci wanda ke nufin barawo yayin da ake masa ihu da zai bar wurin wani taro.

Wadanda suka yada bidiyon sunce abun ya faru ne kwanan nan sanda gwamnan da wasu ‘yan jam’iyar All progressives Congress (APC) suka ziyarci polytechnic din jihar Kwara domin gudanar da taro na siyasa.

An tura bidiyon a wani shafin Facebook, Peter Obi Support Group, a rananr Litinin inda sama da mutane 2,600 suka kalla.

Wani shafi mai suna Nigeria Youth Movement shima ya tura bidiyon tare da rubutun:”Mutanen da suka bar APC zuwa PDP na koran gwamnan jihar Kwara, suna ihun sai Buky Bukola Saraki”. Mutane sama da 1,200 sun kalla bidiyon da aka tura shi ranan Talata.

Banda Facebook, an tura bidiyon zuwa Youtube, Whatsapp da TikTok.

Wani shafin Youtube, E-vibez TV, daya tura bidiyon ranan Litinin, yace Abdulrazaq na kokarin yin camfen na karin zaben sa a shekarar 2023. A shafin, sama da mutane 7,900 suka kalli bidiyon.

Tabbatarwa

TheCable ta saka bidiyon a InVID, na’uran gudanar da bincike a yanar gizo inda yanuna cewa farko bidiyon an tura shi a Youtube a shekarar 2018.

Bidiyon an fara tura shi ne a Youtube a shafin, Kwara Fist, a ranar 25 ga watan Disamba 2018, tare da rubutun: “An samu barkewan rikici a Ilorin a wurin taro na 53 na shekara shekara na Ilorin Emirate Progressive Descendent Union (IEPDU) sanda magoya bayan shugaban majalisar dattawa, Dr. Bukola Saraki suka kwace ragamar gudanar da taron”.

A ranar 9 ga watan Agusta, gwamnatin jihar Kwara tayi magana a game da bidiyon a wata sanarwa data daura a shafin ta na Facebook.

Sanarwan da Bashir Adigun, mataimakin gwamnan akan hulda da jama’a akan harkan siyasa, da aka yi wa taken: “Bidiyon karya akan gwamna AbdulRazaq: Tunatarwa akan rashin ci gaban Kwara”.

Adigun yace Bidiyon an dauke shi ne a ranar 26 ga watan Disamban 2018, sanda ‘yan daba da kuma magoya bayan Bukola Saraki, tsohon shugaban majalisar dattijai, ya yi gargadi a taron da Ilorin Emirate Descendents Progressive Union (IEDPU).

Adigun ya ce bidiyon an dauke shi ne sanda gwamnan yana dan takaran gwamna a jihar inda ya halarci taro a matsayin babban bako a garin da ya fito.

Ya kara da cewa babu wani taro daya gudana a makarantan Polytechnic na Kwara a ranar 7 ga watan Agusta, da zai iya nuna cewa gwamnan ya harci taron.

“Wadanda suka turo bidiyon sunyi shi ne da niyyan a ce ana yi wa gwamna mai mulki ihu,” inji shi.

Hukunci

Bidiyon dake nuna dandazon jama’a nayi wa gwamnan jihar Kwara ihu na yaudara ne. Tsohon bidiyo ne da aka dauke shi tun shekarar 2018. Ba sabon bidiyo bane da aka dauka kwanan nan.

TAGGED: Abdulrahman Abdulrazaq, bukola saraki, Fact Check, Ilorin, Kwara State

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi August 17, 2022 August 17, 2022
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

Rárá, Nàìjíríà kò fi àwọn ọmọ iṣẹ́ ológun rán sẹ sí Ísírẹ́lì láti dá rògbòdìyàn tó ń ṣẹlẹ̀ níbẹ̀ dúró

Ìròyìn lati inú fídíò Facebook kan sọ pé Nàìjíríà fi àwọn ọmọ ogun ránṣẹ́ sí…

June 28, 2025

Ḿbà, Naijiria ézipụ̀ghị̀ ńdị́ ágha ńkwàdó ùdó nà òbòdò Isreal

Ótù ihe ngosị si na Facebook kwuru na Naijiria zipụrụ ndị agha ka ha gaa…

June 28, 2025

No, Nigeria no send peace support mission go Israel

One Facebook video claim sey Nigeria send soldiers go Israel for joint peace support mission.…

June 28, 2025

A’a, Najeriya ba ta tura tawagar taimakon zaman lafiya zuwa Isra’ila ba

Wani faifan bidiyo na Facebook ya nuna cewa Najeriya ta tura dakaru domin aikin hadin…

June 28, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Rárá, Nàìjíríà kò fi àwọn ọmọ iṣẹ́ ológun rán sẹ sí Ísírẹ́lì láti dá rògbòdìyàn tó ń ṣẹlẹ̀ níbẹ̀ dúró

Ìròyìn lati inú fídíò Facebook kan sọ pé Nàìjíríà fi àwọn ọmọ ogun ránṣẹ́ sí orílẹ̀ èdè Ísírẹ́lì kí rògbòdìyàn…

CHECK AM FOR WAZOBIA
June 28, 2025

Ḿbà, Naijiria ézipụ̀ghị̀ ńdị́ ágha ńkwàdó ùdó nà òbòdò Isreal

Ótù ihe ngosị si na Facebook kwuru na Naijiria zipụrụ ndị agha ka ha gaa kwàdó udo na mba Isreal.…

CHECK AM FOR WAZOBIA
June 28, 2025

No, Nigeria no send peace support mission go Israel

One Facebook video claim sey Nigeria send soldiers go Israel for joint peace support mission. One male broadcaster wey dey…

CHECK AM FOR WAZOBIA
June 28, 2025

A’a, Najeriya ba ta tura tawagar taimakon zaman lafiya zuwa Isra’ila ba

Wani faifan bidiyo na Facebook ya nuna cewa Najeriya ta tura dakaru domin aikin hadin gwiwa na tallafawa zaman lafiya…

CHECK AM FOR WAZOBIA
June 28, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?