TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: Bello el-Rufai yayi kuskure. Hadiza Balarabe ba ita ce mataimakiyar gwamna mace ta farko ba a Najeriya
Share
Latest News
Amupitan, ẹni tí Ààrẹ Nàìjíríà ṣẹ̀ṣẹ̀ yàn gẹ́gẹ́bí alága tuntun fún INEC kò sí lára àwọn agbẹjọ́rò fún Tinubu ní ilé ẹjọ́ ìbò
Amupitan, wanda INEC ta zaba, ba ya cikin tawagar lauyoyin Tinubu a kotun zabe
Amupitan, INEC chair nominee, bin no dey inside Tinubu legal team for election tribunal
FACT CHECK: Viral video showing ‘Boko Haram taking over army barracks’ NOT from Nigeria
FACT CHECK: Amupitan, INEC chair nominee, wasn’t part of Tinubu’s legal team at election tribunal
Anambra guber: Offences that can get you arrested during elections in Nigeria
Charly Boy yayi da’awar karya kan cewa Dan Nnamdi Kanu yaci gasar ‘kwakwalwa ta Duniya’
Charly Boy no tok true sey Nnamdi Kanu son win ‘international brain competition’
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

Bello el-Rufai yayi kuskure. Hadiza Balarabe ba ita ce mataimakiyar gwamna mace ta farko ba a Najeriya

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published March 23, 2024 4 Min Read
Share

Bello el-Rufai, mai wakiltar Kaduna ta arewa a majalisar tarayya, yace Hadiza Balarabe ce mace ta farko da aka zaba a matsayin mataimakiyar gwamna a Najeriya.

Danmajalisan yayi maganan ne a wani shiri da yayi da Seun Okinbaloye, wani babban dan jarida.

Shirin nada mabiya 16,300, mutane 94,760 sun gani, 602 sunyi sharhi a kai sannan 2,900 sun danna alaman so a kai.

Bello da ne ga Nasir el-Rufai, tsohon gwamnan jihar Kaduna.

A 2018, Nasir el-Rufai ya dauka Balarabe a matsayin mataimakiyar sa a zaben gwamnan 2019.

Yace ya dauka Balarabe ne saboda Barnabas Bantex, matainakinsa na lokacin, ya sanar da shi cewa zai yi takaran zama sanata.

Kafun ta zama mataimakiyar el-Rufai, Balarabe be shugaban cibiyoyin kiwon lafia na Kaduna.

TABBATARWA

Da yake magana a kan ayyukan da baban shi yayi a Kaduna, danmajalisan yace baban shi, ta Balarabe ya gyara duka cibiyoyin kiwon lafia 255 da ke jihar.

“Daya daga cikin abubuwan da babana yayi tare da mataimakiyar sa, Dr. Hadiza (Balarabe), wanda itace mataimakiyar gwamna mace ta farko da aka zaba a Najeriya shine gyara duka cibiyoyin kiwon lafia 255 dake Kaduna,” inji dan majalisar.

Saidai, bincike da TheCable tayi ya nuna tun da a ka dawo dimokradiya a 1999, Najeriya ta samu mataimakan gwamna mata banda Balarabe.

MATA DA SUKA YI MATAIMAKAN GWAMNA

Jihar Legas ne na farko a zaben mace a matsayin mataimakiyar gwamna. A 1992, a lokacin da a aka yi mulkin dimokradiya na wani dan kankanin lokaci, Micheal Otedola ya zama gwamnan Legas a karkashin National Republic Convention (NRC) tare da Sinatu Ojikutu a mataimakiyar sa.

Ojikutu yayi gwamna har zuwa Nuwamban 1993 da aka yi juyin mulki.

A 1999, Najeriya ta koma mulkin dimokradiya. Bola Tinubu ya lashe zaben gwamnan jihar Legas a karkashin jam’iyar Alliance for Democracy (AD) tare da Kofoworola Akerele-Bucknor a mataimakiyar sa.

Tun daga lokacin, irin su Adebisi Sosan, Adejoke Orelope-Adefurile, da Oluranti Adebule duk sun yi mataimakan gwanma a Legas tsakanin 2007 da 2019.

Abiodun Olumiji tayi ma Ayo Fayose mataimakiyar gwamna daga Satumban 2005 zuwa 2006. Funmilayo Olayinka tayi ma Kayode Fayemi mataimakiya daga 2010 zuwa 2013 inda ta mutu sannan Modube Adelabu ta zama mataimakiyar gwamna a 2013.

A jihar Ogun, Salimat Badru tayi mataimakiyar gwamna daga 2003 zuwa 2011, sannan Yetunde Onanuga tayi mataimakiyar gwamna a jihar daga 2015 zuwa 2019.

A Osun, Olusa Obada tayi mataimakiyar gwamna daga 2003 zuwa 2010 lokacin mulkin Olagunsoye Oyinlola, sannan Titilayi Laoye-Tomori ta zama mataimakiyar gwamnan jihar daga 2010 zuwa 2018.

Pauline Tallen ta zama mataimakiyar gwamna a jihar Filato a 2007, inda ta zama mataimakiyar gwamna mace ta farko a arewacin Najeriya sannan Ipalibo Banigo tayi ma Nyesom Wike mataimakiya a jihar Ribas daga 2015 zuwa 2023.

Cecilia Ezeilo tayi ma Ifeanyi Ugwuanyi mataimakiyar gwamna bayan yaci zabe a 2015.

Noimot Salako-Oyedele ta zama mataimakiyar Dapo Abiodun a jihar Ogun a 2019, shekarar da aka rantsar da Balarabe a matsayin mataimakiyar gwamnan Kaduna.

A 2022, an zaba Balarabe a matsayin mataimakiyar Uba Sani. A Maris na 2023, an sake zaben ta a matsayin mataimakiyar gwamna.

HUKUNCI

Maganar da Bello el-Rufai yayi cewa Balarabe mataimakiyar gwamna mace ta farko da a ka zaba a Najeriya ba dai-dai bane.

Sinatu Ojikutu ce mataimakiyar gwamna mace ta farko da a ka zaba.

TAGGED: Bello el-Rufai, elected, Hadiza Balarabe

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi April 8, 2024 March 23, 2024
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

Amupitan, ẹni tí Ààrẹ Nàìjíríà ṣẹ̀ṣẹ̀ yàn gẹ́gẹ́bí alága tuntun fún INEC kò sí lára àwọn agbẹjọ́rò fún Tinubu ní ilé ẹjọ́ ìbò

Àwọn ènìyàn kan tí wọ́n ń lo àwọn ohun ìgbàlódé íbaraẹnise orí ayélujára sọ pé…

October 15, 2025

Amupitan, wanda INEC ta zaba, ba ya cikin tawagar lauyoyin Tinubu a kotun zabe

Wasu masu amfani da shafukan sada zumunta sun yi ikirarin cewa Joash Amupitan, sabon shugaban…

October 15, 2025

Amupitan, INEC chair nominee, bin no dey inside Tinubu legal team for election tribunal

Some social media users claim sey Joash Amupitan, di newly nominated chairman of di Independent…

October 15, 2025

FACT CHECK: Viral video showing ‘Boko Haram taking over army barracks’ NOT from Nigeria

A social media post has attributed certain individuals dressed in camouflage to Boko Haram militants…

October 15, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Amupitan, ẹni tí Ààrẹ Nàìjíríà ṣẹ̀ṣẹ̀ yàn gẹ́gẹ́bí alága tuntun fún INEC kò sí lára àwọn agbẹjọ́rò fún Tinubu ní ilé ẹjọ́ ìbò

Àwọn ènìyàn kan tí wọ́n ń lo àwọn ohun ìgbàlódé íbaraẹnise orí ayélujára sọ pé Joash Amupitan, alága tuntun fún…

CHECK AM FOR WAZOBIA
October 15, 2025

Amupitan, wanda INEC ta zaba, ba ya cikin tawagar lauyoyin Tinubu a kotun zabe

Wasu masu amfani da shafukan sada zumunta sun yi ikirarin cewa Joash Amupitan, sabon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta…

CHECK AM FOR WAZOBIA
October 15, 2025

Amupitan, INEC chair nominee, bin no dey inside Tinubu legal team for election tribunal

Some social media users claim sey Joash Amupitan, di newly nominated chairman of di Independent National Electoral Commission (INEC), bin…

CHECK AM FOR WAZOBIA
October 15, 2025

Charly Boy yayi da’awar karya kan cewa Dan Nnamdi Kanu yaci gasar ‘kwakwalwa ta Duniya’

Charly Boy, mawakin Najeriya, ya yi ikirarin cewa dan Nnamdi Kanu, shugaban kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB), yaci…

CHECK AM FOR WAZOBIA
October 7, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?