TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: Bello el-Rufai yayi kuskure. Hadiza Balarabe ba ita ce mataimakiyar gwamna mace ta farko ba a Najeriya
Share
Latest News
Did Tinubu attend same school as Alexander Zingman? Here is what we know
FACT CHECK: No, Nigeria didn’t deploy peace support mission to Israel
FACT CHECK: Did lawmakers skip the national anthem during Tinubu’s Democracy Day speech?
FACT CHECK: Did a military coup oust Paul Biya as Cameroon’s president?
FACT CHECK: Ndume erred. 22 governors didn’t endorse Jonathan in 2015
Rárá, Pope Leo kò bẹ Tinubu kó tú Nnamdi Kanu sílẹ̀ ní àtìmọ́lé
Ḿbà, Pope Leo áyọghị Tinubu kà ọ́ tọ́pụ̀ Nnamdi Kanu nà ǹgá
No, Pope Leo no beg Tinubu to release Nnamdi Kanu
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

Bello el-Rufai yayi kuskure. Hadiza Balarabe ba ita ce mataimakiyar gwamna mace ta farko ba a Najeriya

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published March 23, 2024 4 Min Read
Share

Bello el-Rufai, mai wakiltar Kaduna ta arewa a majalisar tarayya, yace Hadiza Balarabe ce mace ta farko da aka zaba a matsayin mataimakiyar gwamna a Najeriya.

Danmajalisan yayi maganan ne a wani shiri da yayi da Seun Okinbaloye, wani babban dan jarida.

Shirin nada mabiya 16,300, mutane 94,760 sun gani, 602 sunyi sharhi a kai sannan 2,900 sun danna alaman so a kai.

Bello da ne ga Nasir el-Rufai, tsohon gwamnan jihar Kaduna.

A 2018, Nasir el-Rufai ya dauka Balarabe a matsayin mataimakiyar sa a zaben gwamnan 2019.

Yace ya dauka Balarabe ne saboda Barnabas Bantex, matainakinsa na lokacin, ya sanar da shi cewa zai yi takaran zama sanata.

Kafun ta zama mataimakiyar el-Rufai, Balarabe be shugaban cibiyoyin kiwon lafia na Kaduna.

TABBATARWA

Da yake magana a kan ayyukan da baban shi yayi a Kaduna, danmajalisan yace baban shi, ta Balarabe ya gyara duka cibiyoyin kiwon lafia 255 da ke jihar.

“Daya daga cikin abubuwan da babana yayi tare da mataimakiyar sa, Dr. Hadiza (Balarabe), wanda itace mataimakiyar gwamna mace ta farko da aka zaba a Najeriya shine gyara duka cibiyoyin kiwon lafia 255 dake Kaduna,” inji dan majalisar.

Saidai, bincike da TheCable tayi ya nuna tun da a ka dawo dimokradiya a 1999, Najeriya ta samu mataimakan gwamna mata banda Balarabe.

MATA DA SUKA YI MATAIMAKAN GWAMNA

Jihar Legas ne na farko a zaben mace a matsayin mataimakiyar gwamna. A 1992, a lokacin da a aka yi mulkin dimokradiya na wani dan kankanin lokaci, Micheal Otedola ya zama gwamnan Legas a karkashin National Republic Convention (NRC) tare da Sinatu Ojikutu a mataimakiyar sa.

Ojikutu yayi gwamna har zuwa Nuwamban 1993 da aka yi juyin mulki.

A 1999, Najeriya ta koma mulkin dimokradiya. Bola Tinubu ya lashe zaben gwamnan jihar Legas a karkashin jam’iyar Alliance for Democracy (AD) tare da Kofoworola Akerele-Bucknor a mataimakiyar sa.

Tun daga lokacin, irin su Adebisi Sosan, Adejoke Orelope-Adefurile, da Oluranti Adebule duk sun yi mataimakan gwanma a Legas tsakanin 2007 da 2019.

Abiodun Olumiji tayi ma Ayo Fayose mataimakiyar gwamna daga Satumban 2005 zuwa 2006. Funmilayo Olayinka tayi ma Kayode Fayemi mataimakiya daga 2010 zuwa 2013 inda ta mutu sannan Modube Adelabu ta zama mataimakiyar gwamna a 2013.

A jihar Ogun, Salimat Badru tayi mataimakiyar gwamna daga 2003 zuwa 2011, sannan Yetunde Onanuga tayi mataimakiyar gwamna a jihar daga 2015 zuwa 2019.

A Osun, Olusa Obada tayi mataimakiyar gwamna daga 2003 zuwa 2010 lokacin mulkin Olagunsoye Oyinlola, sannan Titilayi Laoye-Tomori ta zama mataimakiyar gwamnan jihar daga 2010 zuwa 2018.

Pauline Tallen ta zama mataimakiyar gwamna a jihar Filato a 2007, inda ta zama mataimakiyar gwamna mace ta farko a arewacin Najeriya sannan Ipalibo Banigo tayi ma Nyesom Wike mataimakiya a jihar Ribas daga 2015 zuwa 2023.

Cecilia Ezeilo tayi ma Ifeanyi Ugwuanyi mataimakiyar gwamna bayan yaci zabe a 2015.

Noimot Salako-Oyedele ta zama mataimakiyar Dapo Abiodun a jihar Ogun a 2019, shekarar da aka rantsar da Balarabe a matsayin mataimakiyar gwamnan Kaduna.

A 2022, an zaba Balarabe a matsayin mataimakiyar Uba Sani. A Maris na 2023, an sake zaben ta a matsayin mataimakiyar gwamna.

HUKUNCI

Maganar da Bello el-Rufai yayi cewa Balarabe mataimakiyar gwamna mace ta farko da a ka zaba a Najeriya ba dai-dai bane.

Sinatu Ojikutu ce mataimakiyar gwamna mace ta farko da a ka zaba.

TAGGED: Bello el-Rufai, elected, Hadiza Balarabe

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi April 8, 2024 March 23, 2024
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

Did Tinubu attend same school as Alexander Zingman? Here is what we know

During the launch of the renewed hope mechanisation programme in Abuja on Monday, President Bola…

June 24, 2025

FACT CHECK: No, Nigeria didn’t deploy peace support mission to Israel

A Facebook video purports that Nigeria deployed troops for a joint peace support mission in…

June 24, 2025

FACT CHECK: Did lawmakers skip the national anthem during Tinubu’s Democracy Day speech?

A viral X post claims that Nigeria’s new national anthem was not recited during the…

June 13, 2025

FACT CHECK: Did a military coup oust Paul Biya as Cameroon’s president?

Reports of a military coup in Cameroon ousting President Paul Biya have gone viral on…

June 13, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Rárá, Pope Leo kò bẹ Tinubu kó tú Nnamdi Kanu sílẹ̀ ní àtìmọ́lé

Ẹni kan tí ó ń lo Facebook, ohun ìgbàlódé ibaraẹnisọrẹ orí ayélujára sọ pé Robert Francis Prevost, Pope Leo XIV…

CHECK AM FOR WAZOBIA
June 10, 2025

Ḿbà, Pope Leo áyọghị Tinubu kà ọ́ tọ́pụ̀ Nnamdi Kanu nà ǹgá

Ótù onye na Facebook ekwuola na Pope Leo na ụfọdụ ndị Bishop yọrọ onye isiala Bola Tinubu ka ọ tọpụ…

CHECK AM FOR WAZOBIA
June 10, 2025

No, Pope Leo no beg Tinubu to release Nnamdi Kanu

One Facebook user claim sey Pope Leo XVI and oda bishops join mouth beg President Bola Tinubu to release Nnamdi…

CHECK AM FOR WAZOBIA
June 10, 2025

A’a, Paparoma Leo bai nemi Tinubu ya saki Nnamdi Kanu ba

Wani mai amfani da Facebook ya yi ikirarin cewa Paparoma Leo na 16 da wasu limaman coci sun roki shugaban…

CHECK AM FOR WAZOBIA
June 10, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?