TheCable Fact Check
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Reading: Bidiyon shugaban kasar Zambiya ya na cewa ba zai tsaya takara ba na bogi ne
Share
Latest News
Ị́hé ńgósị́ ébé ńdị́ ụ́ká Naijiria jị́ égbè n’ụ́lọ́ ụ́ká ézị́ghị́ézị́
Hotunan da ke yawo na kiristocin Najeriya rike da makamai a coci suna yaudarar
Àwọn fọ́tò tó sàfihàn àwọn ọmọ Nàìjíríà ẹlẹ́sìn Kristẹni tí wọ́n di nnkan ìjà mọ́ra kò seé gbàgbọ́
Viral foto wey show as Nigerian Christians dey cari gun for church dey mislead pipu
FACT CHECK: Viral photos of Nigerian Christians bearing arms in churches are misleading
Da’awar cewa Davido da Chioma suna tsammanin ɗansu na uku karya ne
Òótọ́ kọ́ ni ọ̀rọ̀ tó sọ pé Davido àti Chioma ń gbaradì fún ọmọ wọn kẹta
Evidence no dey sey Davido and Chioma dey expect dia third pikin
Advertisement
Aa
TheCable Fact CheckTheCable Fact Check
Search
  • Home
  • Fact Check
  • Fake News
  • Check Am For Wazobia
Follow US

Bidiyon shugaban kasar Zambiya ya na cewa ba zai tsaya takara ba na bogi ne

Ahmad Sahabi
By Ahmad Sahabi Published October 18, 2023 4 Min Read
Share

Jam’iyar United Party for National Development (UNDP) tayi watsi da wani bidiyo dake yawo dake nuna shugaba Hakainde Hichilema na Zambiya ya na cewa ba zai sake tsaya wa takara ba a zaben 2026.

A bidyon da ke ta yawo, ana iya ganin Hichilema sanye da kwat tare da tutar kasar Zambiya a bayan sa, ya na bayyana cewa ba zai nema yin tazarce ba a zaben da za a gudanar da kasar a 2026.

“Ina so shaida cewa ina sane da kalubalen da aka fuskanta a karkashin mulki na a matsayi na na shugaban wannan kasa mai albarka. Ina so na sanar da cewa ba zan yi takara ba a zaben da za ayi a 2026. A tunani na, wannan hukuncin dana dauka shine yafi don ci gaban kasar mu,” inji shi.

Hichilema yayi takaran shugaban kasa so biyar bai ci ba kafun yayi nasara daga baya a 2021.

A Zambiya, ana zaben shugaban kasa yayi shekaru 5 yana mulki kuma wa’adi biyu.

Idan aka ma bidiyo kallo na kusa-kusa, za aga motsin bakin da fitar maganar sa ba a tare suke tafiya ba, sannan bayan bidiyon yayi dishi-dishi. Ta nan za a gane anyi amfani da artificial intelligence (AI) a hada bidiyon.

Bidiyon na zuwa ne a lokacin da siyasar kasar Zambiya ke daukan zafi kafun zaben da za ayi a kasar a 2026.

Kamar yadda ake yi a sauran kasashe, idan lokacin zabe ya gabato, ana yawan yada bidiyoyi na karya don a yaudari mutane ko chanza musu tunani akan wadansu ‘yan takara.

A wata sanarwa da Batuke Imenda, sakatare janar na jam’iyar UPND mai mulki a Zambiya, ya zargi “yan bata gari” da “hadawa tare da yada bidiyoyi na karya da akayi amfani da muryar shugaban kasar da manufar a yaudari jama’a”.

“Mun fahimci wannan aiki ne na ‘yan adawa. Gaggawarsu har ya kai ga sun fara niyyan aikata laifi a kan shugaban da ‘yan kasa suka zaba,” inji sanarwar.

“Mun san wasu shuagabannin ‘yan adawa suna nan suna ta kokarin yin abubuwa da zasu janyo ma gwamnati mai mulki tarzoma.

“Mun san kuna neman mabiya ne kuma ku samu karbuwa amma zamu tunatar daku cewa doka makaho ne.

“Ba boyeyyen abu bane cewa wasu daga cikin ku suna abubuwan da suka sabawa doka don janyo hankalin jami’an tsaro. Sannan da zarar an kama ku don yin bincike, kune kuka fi kowa ihu.

“Jam’iyar tana so tayi kira ga duk wanda keda hannu a wannan bidiyon da ke ta yawo cewa zai kwashi kashin shi a hannu idan hukuma ta kama shi.”

Shugaban kasar bai ce komai ba har yanzu a game da bidiyon.

Saidai, rundunar ‘yan sandan kasar sunce sun fara bincike don gano wadanda suka hada bidiyon don a kama su kuma a hukuntasu.

TAGGED: AI-generated disinformation, Hakainde Hichilema, Hausa FactCheck, Zambia

Please send your feedback, claims to fact check and corrections requests to [email protected]

Ahmad Sahabi October 18, 2023 October 18, 2023
Share this Article
Facebook Twitter Email Copy Link Print
Leave a comment Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

POPULAR POSTS

Advertisement

Ị́hé ńgósị́ ébé ńdị́ ụ́ká Naijiria jị́ égbè n’ụ́lọ́ ụ́ká ézị́ghị́ézị́

Ka ndị omekome wakpochara ndị gara ụka na Christ Apostolic Church (CAC) dị na Oke…

December 4, 2025

Hotunan da ke yawo na kiristocin Najeriya rike da makamai a coci suna yaudarar

Biyo bayan harin da wasu ‘yan bindiga suka kai kan mabiya cocin Christ Apostolic Church…

December 4, 2025

Àwọn fọ́tò tó sàfihàn àwọn ọmọ Nàìjíríà ẹlẹ́sìn Kristẹni tí wọ́n di nnkan ìjà mọ́ra kò seé gbàgbọ́

Lẹ́hìn ìgbà tí àwọn oníwà jàgídíjàgan kan kọlu àwọn ènìyàn tí wọ́n ń jọ́sìn ní…

December 4, 2025

Viral foto wey show as Nigerian Christians dey cari gun for church dey mislead pipu

Afta bandits attack worshippers Christ Apostolic Church (CAC) branch for Oke Isegun inside di Eruku…

December 4, 2025
Advertisement
Advertisement

YOU MAY ALSO LIKE

Ị́hé ńgósị́ ébé ńdị́ ụ́ká Naijiria jị́ égbè n’ụ́lọ́ ụ́ká ézị́ghị́ézị́

Ka ndị omekome wakpochara ndị gara ụka na Christ Apostolic Church (CAC) dị na Oke Isegun n'obodo Eruku nke Kwara…

CHECK AM FOR WAZOBIA
December 4, 2025

Hotunan da ke yawo na kiristocin Najeriya rike da makamai a coci suna yaudarar

Biyo bayan harin da wasu ‘yan bindiga suka kai kan mabiya cocin Christ Apostolic Church (CAC) a reshen cocin Christ…

CHECK AM FOR WAZOBIA
December 4, 2025

Àwọn fọ́tò tó sàfihàn àwọn ọmọ Nàìjíríà ẹlẹ́sìn Kristẹni tí wọ́n di nnkan ìjà mọ́ra kò seé gbàgbọ́

Lẹ́hìn ìgbà tí àwọn oníwà jàgídíjàgan kan kọlu àwọn ènìyàn tí wọ́n ń jọ́sìn ní ẹ̀ka Christ Apostolic Church (CAC)…

CHECK AM FOR WAZOBIA
December 4, 2025

Viral foto wey show as Nigerian Christians dey cari gun for church dey mislead pipu

Afta bandits attack worshippers Christ Apostolic Church (CAC) branch for Oke Isegun inside di Eruku community for Kwara state on…

CHECK AM FOR WAZOBIA
December 4, 2025

CableCheck seeks to provide reliable tools and resources for readers to tackle the menace of fake and misleading materials constantly pushed into the public space from various sources. We monitor the accuracy of claims made in traditional and social media. We also provide a tracker to hold politicians and policymakers accountable for the plans and promises they make to the public. CableCheck is a project of the Cable Newspaper Journalism Foundation (CNJF), supported by the MacArthur Foundation and implemented by TheCable newspaper.

Follow US: 

LINKS

  • Contact
  • About Us
  • Non-Partisanship Policy
  • Funding
  • Correction Policy
© Copyright TheCable. All Rights reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?